Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 16:12 - Littafi Mai Tsarki

12 Dā ina zamana da salama, Amma Allah ya maƙare ni, Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni. Allah ya maishe ni abin bārata.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 16:12
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ko na yi zunubi ina ruwanka, Kai mai ɗaure mutane? Me ya sa ka maishe ni abin bārata? Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?


Ya sa naman jikina da fatar jikina su lalace, Ya kuma kakkarya ƙasusuwana.


Duk da haka ka ƙi taimakonmu da namomin jejin nan, Ka bar mu a cikin duhu baƙi ƙirin.


waɗanda suka kasai da ransu saboda ni, ba kuwa ni kaɗai nake gode musu ba, har ma da dukkan ikilisiyoyin al'ummai.


Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje. Amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”


Sa'ad da suka riƙe ka, Sai ka karye ka tsattsaga hannuwansu. Sa'ad da suka jingina da kai, Sai ka karye, har ka sa kwankwasonsu ya firgiza.


Sa'ad da fitilarsa take haskaka mini, Ta wurin haskensa kuma nake tafiya da duhu,


Wannan mutum mai girmankai ne, ɗan tawaye.


Shi ya aiko da hadura, suka yi kacakaca da ni, Suka ƙuƙƙuje ni, ga shi kuwa, ba wani dalilin da ya sa ya yi mini rauni.


“Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi? Kana tsammani ni dodon ruwa ne?


Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki, Amma Allah yakan sa su yi tsit, Ya kakkarya haƙoransu.


Ba ni da salama, ba ni da hutawa, Wahala ba za ta taɓa ƙarewa ba.”


Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau, Dafinsu kuwa ya ratsa jikina. Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.


Allah Mai Iko Dukka ya lalatar da ƙarfin halina. Allah ne ya tsorata ni,


Hakika ikonsa ya yi ta gāba da ni dukan yini.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ