Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 14:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Amma ɗan mutum ya mutu, ƙarshensa ke nan, Ya mutu, a ina yake a lokacin nan?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 14:10
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata, A wannan jiki zan ga Allah.


Amma matattu ba za su tashi ba daɗai, Ba za su ƙara tashi ba sam, muddin sararin sama na nan. Sam, ba za a dame su cikin barcinsu ba.


Sa'ad da Yakubu ya gama yi wa 'ya'yansa maza wasiyya, sai ya hau da ƙafafunsa bisa kan gado, Ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa kai shi ga jama'arsa waɗanda suka riga shi.


Nan tāke, ta fāɗi a gabansa, ta mutu. Da dai samarin suka shigo, suka iske ta matacciya, suka ɗauke ta suka fitar da ita, suka binne ta a jikin mijinta.


Sai Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sa'an nan ya săki ransa.


Muguntar mugun takan kawo hallakarsa, amma adalin mutum, an kiyaye shi ta wurin dattakonsa.


Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”


“Ya Allah, me ya sa ka bari aka haife ni? Da ma na mutu tun kafin wani ya gan ni!


“Da ma na mutu tun a cikin cikin uwata, Ko kuwa da haihuwata in mutu.


Gama mu kamar baƙi ne, masu yawo a gabanka kamar kakanninmu. Kwanakinmu a duniya kamar inuwa ne, ba za mu tsere wa mutuwa ba.


Da a ce na mutu a lokacin, da yanzu ina huce,


Da Allah ya bincike ku sosai, Zai iske wani abin kirki ne a cikinku? Kuna tsammani za ku ruɗi Allah, kamar yadda kuke ruɗin mutane?


In aka zuba ruwa, sai ya toho kamar sabon tsiro.


Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba? Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba? Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura, Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”


Amma zai shuɗe kamar ƙura. Waɗanda dā suka san shi, Za su yi mamaki saboda rashin sanin inda ya tafi.


Dukansu wuri ɗaya za su tafi, gama dukansu biyu daga turɓaya suka fito, dukansu biyu kuma za su koma cikinta.


Wa zai iya tabbatarwa, cewa ruhun mutum zai tafi sama, ruhun dabba kuwa zai tafi ƙasa?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ