Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 13:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Na fid da zuciya ɗungum. To, in Allah ya kashe ni, sai me? Zan faɗa masa ƙarata.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 13:15
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ko da hanyan nan ta bi ta tsakiyar duhu na mutuwa, Ba zan ji tsoro ba, ya Ubangiji, Gama kana tare da ni! Sandanka na makiyayi da kerenka Suna kiyaye lafiyata.


Duk da haka Allah ya san kowane irin hali da nake ciki. Idan ya jarraba ni zai tarar ni tsattsarka ne.


duk sa'ad da zuciyarmu ta ba mu laifi, saboda Allah ya fi ta, ya kuma san kome.


Allah ya sawwaƙa in ce kun yi daidai, Har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.


Muguntar mugun takan kawo hallakarsa, amma adalin mutum, an kiyaye shi ta wurin dattakonsa.


A shirye nake in faɗi ƙarata, Domin na sani ina da gaskiya.


Kai kanka za ka sa mini laifi? Za ka kā da ni don kai ka barata?


“Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka? Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.”


“Ina so wanda zai yi roƙo ga Allah domina, Kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.


Amma ban yi wani aikin kama-karya ba, Addu'ata ga Allah kuwa ta gaskiya ce.


Kwanakina sun wuce ba sa zuciya, Sun wuce da sauri kamar ƙoshiyar saƙa.


Ka sani, ba ni da laifi, Ka kuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka.


Amma da Allah nake jayayya, ba da ku ba, Ina so in yi muhawara da shi a kan ƙarar da nake da ita.


Sai Yunusa ya yi addu'a ga Ubangiji Allah a cikin cikin kifin,


Duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, Zan yi murna da Allah Mai Cetona.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ