Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 12:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu, Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi, Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 12:4
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.


“Amma yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a suke mini, Waɗanda iyayensu maza ba su fi karnukan da suke kiwon garken tumakina ba.


Ku ba ni zarafi in yi magana, sa'an nan in na gama ku amsa in kun ga dama.


Yanzu kuwa sun mai da wannan karin magana a kaina. Da mutane suka ji, Suka zo suka yi ta tofa mini yau a fuska.


Na lura da yadda mutane suke yi mini mummunar ba'a.


Mutane sun buɗe baki don su haɗiye ni Suna kewaye ni suna ta marina.


Har wa yau kuma, waɗansu suka sha ba'a da bulala, har ma da ɗauri da jefawa a cikin kurkuku.


Da dai suka ji maganar tashin matattu, sai waɗansu suka yi ba'a, amma waɗansu suka ce, “Game da wannan magana kam, mā sāke jin abin da za ka faɗa.”


Farisiyawa kuwa da yake masu son kuɗi ne, da jin haka, suka yi masa tsaki.


Sai suka yi masa dariyar raini. Shi kuma bayan ya fitar da su duka waje, sai ya ɗauki uban yarinyar, da uwa tata, da kuma waɗanda suke tare da shi, ya shiga inda yarinyar take.


Suka yi wani rawani na ƙaya, suka sa masa a kā, suka danƙa masa sanda a hannunsa na dama, suka kuma durƙusa a gabansa, suna yi masa ba'a suna cewa, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!”


Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji, Zan jira ceton Allahna, Allahna zai ji ni.


“Ka kira ni, ni kuwa zan amsa maka, zan kuwa nuna maka manyan al'amura masu girma da banmamaki, waɗanda ba ka sani ba.”


Ka yi gaskiya, za ka nuna girmamawarka ga Ubangiji, amma idan ka yi rashin gaskiya, ka nuna rashin girmamawa ke nan ga Ubangiji.


Suka wahalshe ni, suka yi mini dariya, Suna hararata da ƙiyayya.


Ina so Allah ya ga hawayena, Ya kuma ji addu'ata.


Ayuba, kana tsammani ba za mu iya ba ka amsa ba? Kana tsammani maganganunka na ba'a Za su sa mu rasa abin da za mu mayar maka?


Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci, Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya.


sai ya ce, “Ku ba da wuri, ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci take yi.” Sai suka yi masa dariyar raini.


Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa.


Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya. Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa.


A shirye nake in faɗi ƙarata, Domin na sani ina da gaskiya.


“Yanzu na zama abin waƙa gare su, Abin ba'a kuma a gare su.


“Wane irin mutum ne kai, Ayuba, Da kake shan raini kamar yadda kake shan ruwa,


“Ya Ubangiji ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu, Ka fi ni ƙarfi, ka kuwa rinjaye ni. Na zama abin dariya dukan yini, Kowa yana ta yi mini ba'a.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ