Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 11:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Da ya faɗa maka hikima tana da fannoni da yawa. Akwai abubuwa waɗanda suka fi ƙarfin ganewar ɗan adam. Duba, Allah ya ƙyale wani ɓangare na laifinka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 11:6
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Bayan wannan dukan abubuwan nan suka same mu saboda mugayen ayyukanmu da zunubanmu masu yawa. Ya Allahnmu, ga shi ma, ka hukunta mu kaɗan bisa ga yawan zunubanmu, ka kuma bar mana wannan ringi.


Ƙaunar Ubangiji ba ta ƙarewa, Haka kuma jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.


wanda a zamanin dā ba a sanar da 'yan adam ba, kamar yadda a yanzu aka bayyana wa manzanninsa tsarkaka da annabawa, ta wurin Ruhu,


Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa, “Zan yi magana da misalai, Zan sanar da abin da yake ɓoye tun farkon duniya.”


Amma akwai Allah a Sama mai bayyana asirai, shi ne ya sanar wa sarki Nebukadnezzar da abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayinka waɗanda suka zo cikin tunaninka, sa'ad da kake kwance bisa gadonka ke nan.


Ko ka taɓa jin shirye-shiryen da Allah ya yi? Ko kai kaɗai kake da hikima a cikin mutane?


Ya kuma ce wa Daniyel, “Hakika, Allahnka, Allahn alloli ne da Ubangijin sarakuna, mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”


Ubangiji yakan amince da waɗanda suke biyayya da shi, Yakan koya musu alkawarinsa.


“Allah yana ta'azantar da kai, Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi? Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi.


Mugun lamirinka shi ne yake magana yanzu, Kana ƙoƙari ka ɓuya a bayan maganganunka na wayo.


Allah mai hikima ne, mai iko, Ba wanda zai iya ja in ja da shi.


“Sanin gaibu na Ubangiji Allahnmu ne, amma abubuwan da aka bayyana namu ne, mu da 'ya'yanmu har abada, don mu kiyaye dukan maganar dokokin nan.”


Yakan yi mana rangwame sa'ad da yake hukunta mu, Ko sa'ad da yake sāka mana saboda zunubanmu da laifofinmu.


“Allah ya ce wa mutane, ‘Duba, tsoron Ubangiji shi ne hikima, Rabuwa da mugunta kuma, ita ce haziƙanci.’ ”


Da ma Allah zai amsa maka, Ya yi magana gāba da kai,


Ko kusa ba haka ba ne, Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne. Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata.


“Amma a kan wannan, Ayuba, ka yi kuskure, zan ba ka amsa, Gama Allah ya fi kowane mutum girma.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ