Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 11:20 - Littafi Mai Tsarki

20 Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 11:20
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba za ku sami zaman lafiya wurin waɗannan al'ummai ba, ko tafin ƙafarku ma ba zai sami wurin hutawa ba. Ubangiji kuma zai sa fargaba a zuciyarku, ya sa idanunku su lalace, ranku zai yi suwu.


“Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba, Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba,


A karin maganar mutanen dā an ce, ‘Kowa ya ci amanar abokinsa saboda kuɗi, 'Ya'yansa sā sha wahala!’


to, ta ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji kansa, shi ne ya fara sanar da shi, waɗanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi,


Ko masu saurin gudu ma ba za su tsere ba, Ƙarfafa za su zama kumamai, Sojoji kuma ba za su iya ceton kansu ba.


Idanunmu sun gaji Da zuba ido a banza don samun taimako, Mun zuba ido Ga al'ummar da ba za ta iya cetonmu ba.


Idan ka zagi iyayenka, za ka mutu kamar fitilar da ta mutu cikin duhu.


Abin da mugun yake tsoro, shi yakan auko masa, amma adali yakan sami biyan bukatarsa.


Na gaji da kira, ina neman taimako, Maƙogwarona yana yi mini ciwo, Idanuna duka sun gaji, Saboda ina zuba ido ga taimakonka.


Ba wani duhu, ko duhu baƙi ƙirin Inda masu aikata mugunta za su ɓuya.


Za ta murɗe su ba tausayi, Hakika za su yi ƙoƙari su tsere daga ikonsa, Sai su yi ƙundumbala.


Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah? Sa'ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa?


Dā yana zaune lafiya, Sai razana ta tatike shi, Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa.


to, zan hukunta ku. Zan aukar muku da bala'i, da cuce-cuce da ba su warkuwa, da zazzaɓin da zai lalatar muku da ido, rai zai zama muku da wahala. Za ku yi shuka a banza gama maƙiyanku ne za su ci.


Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni, Ko ya sake ikonsa ya datse ni!


Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni, Ba wanda zai kiyaye ni, Ba kuwa wanda ya kula da ni.


Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.


Ba mafakar da ta ragu domin makiyaya, Iyayengijin garken ba za su tsira ba.


Sun jira mutuwa, amma ta ƙi samuwa, Sun fi son kabari da kowace irin dukiya.


Ba su da farin ciki, sai sun mutu an binne su tukuna.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ