Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 10:9 - Littafi Mai Tsarki

9 Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni. Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 10:9
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'an nan Ubangiji Allah ya siffata mutum daga turɓayar ƙasa, a cikin kafafen hancinsa kuwa ya hura numfashin rai, mutum kuma ya zama rayayyen taliki.


Amma kai ne Ubanmu, ya Ubangiji. Mu kamar yumɓu ne, kai kuwa kamar maginin tukwane. Kai ka halicce mu,


Za ka yi zuffa da aiki tuƙuru kafin ka sami abinci, har ka koma ƙasa, gama da ita aka siffata ka, kai turɓaya ne, ga turɓaya kuma za ka koma.” (2Tas 3.10; Far 2.7; Zab 90.3; 104.29; M.Had 12.7)


sa'an nan turɓaya ta koma ƙasa kamar a dā, ruhu kuma ya koma wurin Allah wanda ya ba da shi.


“Ya jama'ar Isra'ila, ashe, ba zan yi da ku kamar yadda maginin tukwanen nan ya yi ba? Duba, kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya ku jama'ar Isra'ila.


Ashe, maginin tukwane ba ya iko da yumɓu, ya gina wata domin aiki mai martaba, wata kuma don kasasshen aiki, duk daga curi ɗaya?


Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta, Tukunyar da take daidai da sauran tukwane? Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi? Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta?


Ka tuna da ni sa'ad da za ka taimaki jama'arka, ya Ubangiji! Ka sa ni cikinsu, sa'ad da za ka cece su.


Kakan sa mutane su koma yadda suke, Su zama ƙura.


Ka tuna kwanakin mutum kaɗan ne, ya Ubangiji, Ka tuna yadda ka halicci mutane duka masu mutuwa ne!


Ka kula da wahalata da azabata, Ka gafarta dukan zunubaina.


Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura.


Zan ce kabari shi ne mahaifina, Tsutsotsin da suke cinye ni su ne mahaifiyata, da 'yan'uwana mata.


“Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai, Farin cikina ya riga ya ƙare.


Wannan wadata da muke da ita kuwa, a cikin kasake take, wato, jikunanmu, don a nuna mafificin ikon nan na Allah ne, ba namu ba.


Ta ƙaƙa zai amince da talikinsa wanda aka yi da ƙasa, Abin da yake na ƙura, ana kuwa iya murƙushe shi kamar asu.


Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba? Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba? Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura, Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”


Kai ne ka ba mahaifina ƙarfin da zai haife ni, Kai ne ka sa na yi girma a cikin cikin mahaifiyata.


Duba, ni da kai ɗaya muke a wajen Allah, Dukanmu biyu kuma daga yumɓu aka siffata mu.


Da duk mai rai ya halaka, Mutum kuma ya koma ƙura.


Yakan tuna su mutane ne kawai, Kamar iskar da take hurawa ta wuce.


Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata, In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu, Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.


Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi, Yakan tuna, da ƙura aka yi mu.


Ba wanda ya juyo gare ka ya yi addu'a, ba wanda ya je gare ka neman taimako. Ka ɓuya mana, ka kuwa yashe mu saboda zunubanmu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ