Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 10:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta? Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi? Sa'an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 10:3
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Amma kai ne Ubanmu, ya Ubangiji. Mu kamar yumɓu ne, kai kuwa kamar maginin tukwane. Kai ka halicce mu,


Za ka aikata kowane abu da ka alkawarta mini, Ya Ubangiji, ƙaunarka madawwamiya ce har abada. Ka cikasa aikin da ka fara.


Sa'an nan za ka yi kira, ni kuwa zan amsa, Za ka yi murna da ni, ni talikinka.


Saboda haka, sai duk masu shan wuya bisa ga nufin Allah su danƙa ransu ga Mahalicci mai aminci suna aikata abin da yake daidai.


Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata, Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba.


Kai kanka za ka sa mini laifi? Za ka kā da ni don kai ka barata?


“Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka? Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.”


Ko da yake Allah ne ya arzuta su. Ba na iya gane tunanin mugaye.


Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara, Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.


Allah ya ba da duniya ga mugaye, Ya makantar da dukan alƙalai, Idan ba Allah ne ya yi haka nan ba, to, wa ya yi?


Don haka ban damu da kome ba. Da marar laifin da mai laifin duk, Allah zai hallaka mu.


“Amma daɗai Allah ba zai rabu da amintattu ba, Ba kuwa zai taɓa taimakon mugun mutum ba.


“Da ikonka ne ka yi ni, ka siffata ni, Yanzu kuma da ikon nan naka ne za ka hallaka ni.


Ba ku iya ganin abin da Allah ya yi mini, Ya kafa tarko don ya kama ni.


“Na rantse da Allah Mai Iko Dukka, Wanda ya ƙwace mini halaliyata, Wanda ya ɓata mini rai.


Ka zama mugu a gare ni, Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.


Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa, Ba shi ne ya halicce su ba? Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?


Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai.


Kada fa a manta da cewa, Ubangiji shi ne Allah! Shi ne ya yi mu, mu kuwa nasa ne, Mu jama'arsa ne, mu garkensa ne.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ