Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Amos 9:11 - Littafi Mai Tsarki

11 “Wata rana zan sāke tayar da birnin Dawuda Tankar yadda akan ta da gidan da ya rushe. Zan gyara garunsa, in sāke mai da shi. Zan sāke gina shi in mai da shi kamar yadda yake tun dā.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Amos 9:11
37 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'an nan wani daga cikin zuriyar Dawuda zai zama sarki. Zai mallaki jama'a da aminci da ƙauna. Zai aikata abin da yake daidai da hanzari, zai sa a aikata adalci.


Me ya sa ka rushe shingen da yake kewaye da ita? Ga shi yanzu, duk mai wucewa yana iya satar 'ya'yanta.


Amma suka tuna da zamanin dā, zamanin Musa bawan Ubangiji, suka yi tambaya suka ce, “Yanzu fa, ina Ubangiji yake wanda ya ceci shugabannin jama'arsa daga teku? Ina Ubangiji yake, wanda ya ba Musa iko musamman?


Bayan wannan mutanen Isra'ila za su komo su nemi Ubangiji Allahnsu, da Dawuda, sarkinsu. Da tsoro za su komo zuwa wurin Ubangiji domin alheransa a kwanaki na ƙarshe.


Zan sa mutum da dabba su yawaita a cikinku, su kuma ba da amfani. Zan sa a zauna a cikinku kamar dā, sa'an nan zan nuna muku alheri fiye da dā. Daga nan za ku sani, ni ne Ubangiji.


Dukan itatuwan jeji za su sani, Ni Ubangiji nakan sa manyan itatuwa su zama ƙanana, In sa ƙanana kuma su zama manya, In sa ɗanyen itace ya bushe, In sa busasshen itace kuma ya zama ɗanye, Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.”


Ya Ubangiji, ka komo da mu zuwa gare ka! Mu kuwa za mu koma. Ka sabunta kwanakinmu su zama kamar na dā.


Zan bashe su a hannun waɗanda suke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa.


“Ga abin da zan yi wa gonar inabina. Zan cire shingen da yake kewaye da ita, in rushe bangon da ya kāre ta, in bar namomin jeji su cinye ta, su tattake ta.


Ai, don ka kiyaye shi ne, shi da iyalinsa, da dukan abin da yake da shi. Ka kuma sa wa duk abin da yake yi albarka, ka kuwa ba shi shanun da suka isa su cika dukan ƙasan nan.


Sai ka yi kiwon mutanenka da sandanka, Wato garken mallakarka, Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi A tsakiyar ƙasa mai albarka. Bari su yi kiwo cikin Bashan da Gileyad Kamar a kwanakin dā.


“Baitalami cikin Efrata, Wadda kike 'yar ƙarama a cikin kabilar Yahuza, Amma daga cikinki wani zai fito wanda zai sarauci Isra'ila Wanda asalinsa tun fil azal ne.”


Amma za su bauta mini, ni Ubangiji Allahnsu, da Dawuda sarkinsu, wanda zan tayar musu da shi.”


Na tuna kwanakin baya, Na tuna da dukan abin da ka yi, Na tuna da dukan ayyukanka.


Ka rurrushe garun birninsa, Ka mai da sansaninsa mai kagara kufai.


Za a mallaki Edom, Hakka kuma za a mallaki Seyir abokiyar gābanta, Isra'ila za ta gwada ƙarfi.


Za ku sāke gina tsofaffin kufanku na dā can, za ku sāke kafa tushen zuriya da yawa. Za a kira ku, ‘Masu gyaran abin da ya lalace, masu sāke gyaran gidaje.’ ”


Zan sa wa Isra'ilawa waɗanda suke na kabilar Yahuza albarka, zuriyarsu kuma za su mallaki ƙasata da duwatsuna. Zaɓaɓɓun mutanena waɗanda suke bauta mini za su zauna a can.


A duk kuma lokacin da na ce zan gina, in kafa wata al'umma, ko wani mulki,


“Amma za a sami waɗanda za su tsira daga Dutsen Sihiyona, Dutsen zai zama wuri ne mai tsarki. Jama'ar Yakubu za ta mallaki mallakarta.


Ya maƙiyina, kada ka yi murna a kaina, Gama sa'ad da na fāɗi, zan tashi kuma. Sa'ad da na zauna cikin duhu, Ubangiji zai haskaka ni.


Za a faɗaɗa iyakarka A ranar da za a gina garunka.


Ka kuwa ce masa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, mutumin da sunansa Reshe, zai yi girma a inda yake, zai kuma gina Haikalin Ubangiji.


“Ubangiji zai fara ba mutanen Yahuza nasara, domin kada darajar jama'ar Dawuda da ta mazaunan Urushalima ta fi ta mutanen Yahuza.


Ƙasa dukka za ta zama fili, daga Geba zuwa Rimmon a kudancin Urushalima. Amma Urushalima za ta kasance a kan tudu, za ta miƙe daga Ƙofar Biliyaminu, zuwa wurin da ƙofa ta fari take a dā, har zuwa Ƙofar Kusurwa, sa'an nan ta miƙe daga Hasumiyar Hananel zuwa wuraren matsewar ruwan inabin sarki.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ