Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Amos 6:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Sa'ad da Ubangiji ya ba da umarni, babban gida da ƙarami rushewa za su yi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Amos 6:11
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan murmushe gidajensu na rani da na damuna. Zan hallakar da gidajen da aka ƙawata da hauren giwa, Kowane babban gida kuwa za a rushe shi.”


To, haka maganar da na faɗa take, Ba ta kāsa cika abin da na shirya mata, Za ta yi kowane abin da na aike ta ta yi.


Ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gidajen urushalima. Ya ƙone kowane babban gida.


su fyaɗa ku a ƙasa, ku mutanen birni duka, ba kuma za su bar wani dutse a kan ɗan'uwansa ba a birninku, don ba ku fahimci lokacin da ake sauko muku da alheri ba.”


Gama zan tattara dukan al'ummai su yi yaƙi da Urushalima. Za a ci birnin, a washe gidajen. Za a yi wa mata faɗe. Za a kai rabin mutanen birnin bauta, amma za a bar sauran mutanen a cikin birnin.


Ubangiji ya riga ya yi umarni a kanka cewa, “Sunanka ba zai ci gaba ba, Zan farfashe sassaƙaƙƙun siffofi Da siffofi na zubi daga gidan gumakanka. Zan shirya maka kabari, gama kai rainanne ne.”


“Zan umarta a rairayi jama'ar Isra'ila Da matankaɗi kamar hatsi. Zan rairaye su daga cikin sauran al'umma, Duk da haka ko ƙwaya ɗaya ba za ta salwanta ba.


Na ga Ubangiji na tsaye a wajen bagade. Ya yi umarni, ya ce, “Bugi ginshiƙan Haikali don shirayi duka yă girgiza. Farfasa su, su fāɗi a kan mutane! Sauran mutane kuwa, Zan kashe su a wurin yaƙi. Ba wanda zai tsere, ko ɗaya.


Ubangiji kansa ne ya rantse. Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Ba na son girmankai na jama'ar Isra'ila. Ba na son fādodinsu. Zan ba da birnin da dukan abin da yake cikinsa ga abokan gābansu.”


Samariya za ta ɗauki hakkin zunubinta, Gama ta tayar wa Allahnta. Za a kashe mutanenta da takobi. Za a fyaɗa jariranta a ƙasa, A kuma tsage matanta masu ciki.”


Ubangiji ya kira mayaƙansa masu jin kansu, masu ƙarfin zuciya, domin su yi jahadi, su hukunta wa waɗanda suke fushi da su.


Saboda lalaci ɗaki yakan yi yoyo, sai tsaiko ya lotsa.


Ya ba da umarni, sai fāri suka zo, Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa.


Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwari Suka cika dukan ƙasar.


Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu, Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,


Kun matsa wa talakawa lamba, Kun ƙwace musu abincinsu. Saboda haka kyawawan gidajen nan da kun gina da dutse, Ba za ku zauna a cikinsu ba, Ba kuwa za ku sha ruwan inabin nan Daga kyawawan gonakin inabinku ba.


Edomawa, wato zuriyar Isuwa, sun ce, “An rurrushe garuruwanmu, amma za su sāke gina su.” Sa'an nan Ubangiji zai amsa, ya ce, “To, su gina mana, ai, zan sāke rurrushe su. Mutane za su ce da ƙasarsu, ‘Ƙasar mugaye, da al'ummar da Ubangiji yake fushi da ita har abada.’ ”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ