Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Amos 5:12 - Littafi Mai Tsarki

12 Na san irin zunuban da kuke yi, Da mugayen laifofin da kuka aikata. Kuna wulakanta mutanen kirki, Kuna cin hanci, Kuna hana a yi wa talakawa shari'ar adalci a majalisa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Amos 5:12
39 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kun ƙi wanda ya tsaya a kan adalci, Da mai faɗar ainihin gaskiya a gaban shari'a.


Shugabanninku 'yan tawaye ne, abokan ɓarayi, a koyaushe sai karɓar kyautai suke yi, da rashawa. Amma ba su taɓa kare marayu a ɗakin shari'a, ko su kasa kunne ga ƙarar da gwauraye suka kawo ba, wato matan da mazansu suka mutu.


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”


Amma 'ya'yansa ba su bi gurbin mahaifinsu ba, amma suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi, suka yi ta cin hanci, suka danne gaskiya.


Kun hukunta mai adalci, kun kuma kashe shi, bai kuwa yi muku tsayayya ba.


Ga shi kuwa, zaluncin da kuka yi na hakkin masu girbi a gonakinku yana ta ƙara, kukan masu girbin kuwa ya kai ga kunnen Ubangijin Runduna.


A cikin annabawa wane ne kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun kuma kashe waɗanda suka yi faɗi a kan zuwan Mai Adalcin nan, wanda a yanzu kuka zama maciya amanarsa, da kuma makasansa,


Sun himmantu su aikata abin da yake mugu da hannuwansu. Sarki da alƙali suna nema a ba su hanci, Babban mutum kuma yana faɗar son zuciyarsa, Da haka sukan karkatar da zance.


Shari'ar shugabannin ƙasar ta cin hanci ce. Firistocinta suna koyarwa don neman riba, Haka kuma annabawa suna annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna dogara ga Ubangiji, suna cewa, “Ai, Ubangiji yana tsakiyarmu, Ba masifar da za ta same mu.”


Ko sojojin da suka fi jaruntaka duka ma, Za su gudu tsirara a ran nan.” Ubangiji ne ya faɗa.


Ubangiji bai yarda a danne 'Yan kurkuku na duniya ba.


Gama sun yi wauta a Isra'ila, sun yi zina da matan maƙwabtansu, sun yi ƙarya da sunana, ni kuwa ban umarce su ba. Ni na sani, ni ne kuma shaida, ni Ubangiji na faɗa.”


Na san tunaninsu da ayyukansu. Ina zuwa domin in tattara jama'ar dukan al'ummai. Sa'ad da suka tattaru, za su ga abin da ikona zai yi,


Amma ba da jimawa ba, a rana ɗaya Dukan waɗannan al'amura za su faru. Kome sihirin da za ki yi, Za ki rasa 'ya'yanki, ki kuwa zama gwauruwa.


Kuna iya tsira idan kuna faɗar gaskiya kuna kuma yin abin da yake daidai. Kada ku gwada ikonku don ku cuci talakawa, kada kuwa ku karɓi rashawa. Kada ku haɗa kai da masu shiri su yi kisankai, ko su aikata waɗansu mugayen abubuwa.


Allah zai hallakar da waɗanda suke zambatar waɗansu, da waɗanda sukan hana a hukunta wa masu mugun laifi, da waɗanda sukan yanka ƙarya don a hana wa amintattu samun shari'ar adalci.


Ta haka kuke hana wa talakawa hakkinsu, kuna kuma ƙin yi musu shari'ar gaskiya. Ta haka kuke ƙwace dukiyar gwauraye, wato matan da mazansu suka rasu, da ta marayu.


Amma kukan ƙyale masu laifi waɗanda suka ba ku rashawa, kukan kuwa ƙi yi wa marasa laifi shari'ar gaskiya.


Kada ka ƙwari matalauci don ka fi shi, kada ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari'a.


Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya, Don na ga ina da kafar kuɓuta,


Bo'aza fa ya tafi, ya zauna a dandalin ƙofar gari. Sai ga wani daga cikin waɗanda hakkinsu ne su ɗauki Rut, shi ne kuwa wanda Bo'aza ya ambata, ya iso. Bo'aza kuwa ya ce masa, “Ratso nan, wāne, ka zauna.” Sai ya ratsa, ya zauna.


Sa'ad da yawan masifun nan da wahalan nan suka same su, to, waƙar nan za ta ba da shaida a kansu, gama zuriyarsu ba za ta manta da wannan waƙa ba, gama na san ƙudurin da suke yi kafin in kawo su ƙasar da na rantse zan bayar.”


“Sai ku naɗa alƙalai da shugabanni domin garuruwanku waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku bisa ga kabilanku. Sai su yi wa jama'a shari'a da adalci.


Mai farin ciki ne mutumin da yake da irin waɗannan kibau da yawa! Faufau ba za a ci nasara a kansa ba, Sa'ad da ya kara da maƙiyansa a wurin shari'a.


Waɗansu mutane suna tsammani cin rashawa yakan yi aiki kamar sihiri, sun gaskata zai iya yin kome.


“Kun karya zuciyar adali ta wurin ƙaryarku, ko da yake ni ban karya zuciyarsa ba. Kun ƙarfafa wa mugu gwiwa, don kada ya bar hanyarsa ta mugunta, ya tsira.


Na san Ifraimu, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. Gama Ifraimu ta yi aikin karuwanci, Isra'ila kuma ta ƙazantu.


Zan kashe Sarkin Mowab da shugabannin ƙasar.”


Abin tausayi ne ku da kuke ɓata shari'a, Kuna hana wa mutane hakkinsu.


Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar.


Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari'a.


“Kada ku rasa yin adalci ga matalauci a wurin shari'a.


Saboda zalunci da rashin kula da matalauta, Da ƙwace gidajen da waɗansu suka gina.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ