Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Amos 5:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ku kasa kunne, ku jama'ar Isra'ila, ga waƙar makoki da zan yi a kanku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Amos 5:1
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Sai ka yi makoki domin hakiman Isra'ila,


“Haka ni Ubangiji Mai Runduna na ce, Ku yi tunani, ku kirawo mata masu makoki su zo, Ku aika wa gwanaye fa.”


Zan yi kuka in yi kururuwa saboda tsaunuka, Zan yi kuka saboda wuraren kiwo, Domin sun bushe sun zama marasa amfani. Ba wanda yake bi ta cikinsu. Ba a kuma jin kukan shanu, Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu sun tafi.


“Ku aske gashin kanku, ku zubar da shi. Ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi 'yan zamanin nan, ya rabu da su saboda fushinsa.


A wannan rana za su yi karin magana a kanku, Za su yi kuka da baƙin ciki mai zafi, Su ce, “An lalatar da mu sarai! Ya sāke rabon mutanena, Ya kawar da shi daga gare ni! Ya ba da gonakinmu ga waɗanda suka ci mu da yaƙi.”


Haka Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Za a yi kuka, a yi kururuwa a titunan birninku saboda azaba. Daga ƙauyuka za a kirawo mutane Su zo su yi makokin. Waɗanda suka mutu, tare da masu makoki da aka ijarar da su.


Ku kasa kunne ga wannan, ya ku matan Samariya, Ku da kuka yi ƙiba kamar turkakkun shanu, Ku da kuke wulakanta kasassu, Kuna yi wa matalauta danniya, Kukan umarci mazajenku, Ku ce, “Kawo mini abin sha!”


Jama'ar Isra'ila, ku kasa kunne ga wannan saƙo da Ubangiji ya aiko muku, ya ce, “Na fitar da iyalanku duka daga Masar.


“Wannan ita ce waƙar makokin. 'Yan matan al'ummai za su raira wa Masar da jama'arta duka, ni Ubangiji Allah na faɗa.”


“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir'auna, Sarkin Masar, ka ce, “ ‘Ka aza kanka kamar zaki a cikin al'ummai, Amma kai kada ne a cikin ruwa. Ka ɓullo cikin kogunanka, Ka gurɓata ruwa da ƙafafunka, Ka ƙazantar da kogunansu.’


“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Sarkin Taya, ka ce Ubangiji Allah ya ce, “ ‘Kai cikakke ne, cike da hikima da jamali!


“Ya kai ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.


Za su yi makoki saboda ke, su ce, “ ‘Ke wadda ake zaune cikinki, kin bace daga tekuna, Ya shahararren birni, wanda yake babba a bakin teku, Ke da mazaunan da suke cikinki, kun sa mazaunan gāɓar teku su ji tsoro!


Wuta ta fito daga jikinta Ta cinye rassanta da 'ya'yanta, Don haka ba wani reshe mai ƙarfi da ya ragu, wanda zai zama sandan mulki. Wannan makoki ne, ya kuwa tabbata makoki.’ ”


Irmiya ya ce, “Ya ku mata, ku ji maganar Ubangiji, Ku kasa kunne ga maganar da ya faɗa, Ku koya wa 'ya'yanku mata kukan makoki, Kowacce ta koya wa maƙwabciyarta waƙar makoki,


Ba zan hukunta su saboda waɗannan al'amura ba? Ba zan sāka wa al'umma irin wannan ba?”


“Domin haka ni Ubangiji na ce, ‘Ka tambayi sauran al'umma. Wa ya taɓa jin irin wannan? Budurwa Isra'ila, ta yi mugun abu ƙwarai!


Waɗanda suka yi rantsuwa da gumakan Samariya, Waɗanda suka ce, ‘Na rantse da gunkin Dan, Da ran gunkin Biyer-sheba,’ Irin waɗannan mutane za su fāɗi, Ba za su ƙara tashi ba.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ