Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Timoti 3:11 - Littafi Mai Tsarki

11 da kuma yawan tsanani, da wuyar da na sha, da suka same ni a Antakiya, da Ikoniya, da Listira, wato irin tsanance-tsanancen da na jure. Amma Ubangiji ya kuɓutar da ni daga cikinsu duka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 tsanani, shan wahala, irin abubuwan da suka faru da ni a Antiyok, Ikoniyum da kuma Listira, tsananin da na jure. Duk da haka Ubangiji ya cece ni daga dukansu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Timoti 3:11
43 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mutumin kirki yakan sha wahala da yawa, Amma Ubangiji yakan cece shi daga cikinsu duka.


Amma da Yahudawa suka ga taro masu yawa, suka yi kishi gaya, suka yi ta musun abubuwan da Bulus ya faɗa, suna zaginsa.


ashe kuwa, Ubangiji ya san yadda zai kuɓutar da masu tsoronsa daga gwaje-gwaje, ya kuma tsare marasa adalci a kan jiran hukunci, har ya zuwa ranar shari'a,


Na sha fama, famar gaske, na gama tseren, na riƙe bangaskiya.


Da na sami taimakon Allah kuwa, ga ni a nan har yanzu, ina shaida wa babba da yaro, ba na faɗar kome sai abin da annabawa da Musa suka ce zai auku,


Zan tsirar da kai daga jama'ar nan da kuma al'ummai, waɗanda zan aike ka a gare su,


Da gardamar ta yi tsanani, don gudun kada su yi kaca-kaca da Bulus, shugaban ya umarci sojan su sauka su ƙwato shi daga wurinsu ƙarfi da yaji, su kawo shi a kagarar soja.


ina bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali'u, har da hawaye, da gwaggwarmaya iri iri da na sha game da makircin Yahudawa.


Amma suka wuce gaba daga Bariyata, suka tafi Antakiya ta ƙasar Bisidiya. Ran Asabar kuma sai suka shiga majami'a suka zauna.


Domin zan sanar da shi yawan wuyar da lalle zai sha saboda sunana.”


Yakan yi ceto, yakan kuma kuɓutar, Yana aikata alamu da mu'ujizai a sama da duniya. Shi ne wanda ya ceci Daniyel daga bakin zakoki.”


Za su yi gāba da kai, amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, ni Ubangiji na faɗa.”


Sa'ad da kuke bi ta cikin ruwa mai zurfi, Zan kasance tare da ku, Wahala ba za ta fi ƙarfinku ba. Sa'ad da kuke bi ta cikin wuta, ba za ku ƙuna ba, Wuyar da ta same ku ba za ta cuce ku ba.


Ubangiji ya ce, “Isra'ila, ku kima ne marasa ƙarfi kuma, Kada ku ji tsoro, zan taimake ku. Ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ni ne mai fansarku.


Kada ka ji tsoro, ina tare da kai, Ni ne Allahnka, kada ka bar kome ya firgita ka. Zan sa ka yi ƙarfi, in kuma taimake ka, Zan kiyaye ka, in cece ka.


Allah ya ce, “Zan ceci waɗanda suke ƙaunata, Zan kiyaye waɗanda suka san ni.


Yakan taimake su, yă kuɓutar da su, Yakan cece su daga mugaye, Gama sukan zo wurinsa don yă kāre su.


Ya kuɓutar da ni daga hannun maƙiya. Kai, ya Ubangiji, ka ba ni nasara a kan maƙiyana, Ka tsare ni daga mutane masu zafin hali.


Wannan waƙa Dawuda ya raira wa Ubangiji sa'ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun Saul da dukan sauran abokan gābansa, ya ce,


Mala'ikan da ya fanshe ni Daga dukan mugunta, Ya sa wa samarin albarka, Bari a dinga ambatarsu da sunana, Da sunan Ibrahim da na Ishaku iyayena, Bari kuma su riɓaɓɓanya, su zama taron jama'a a tsakiyar duniya.”


To, a Listira akwai wani mutum a zaune, wanda ƙafafunsa ba su da ƙarfi, gurgu ne tun da aka haife shi, bai ma taɓa tafiya ba.


domin in tsira daga maƙiyan bangaskiya a Yahudiya, don kuma gudunmawar da nake kaiwa Urushalima, ta zama abar karɓa ga tsarkaka,


Domin kuwa kamar yadda muke shan wuya ƙwarai, irin wadda Almasihu ya sha, haka kuma ake yi mana ta'aziyya ƙwarai, ta wurin Almasihu.


Sa zuciyarmu a kanku ƙaƙƙarfa ce, domin mun sani, kamar yadda kuka yi tarayya da mu a cikin shan wuya, haka kuma, za ku yi tarayya a cikin ta'aziyyar.


Saboda haka, ina murna da raunanata, da cin mutuncin da ake yi mini, da shan wuya, da shan tsanani, da masifu saboda Almasihu, don sa'ad da nake rarrauna, a sa'an nan ne nake da ƙarfi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ