Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Tarihi 32:21 - Littafi Mai Tsarki

21 Ubangiji kuwa ya aiki mala'ika wanda ya karkashe manyan jarumawa, da sarakunan yaƙi, da shugabanni, da kowane riƙaƙƙen soja, da sarkin yaƙi da yake a sansanin Sarkin Assuriya. Sai ya koma ƙasarsa cike da kunya. Sa'ad da ya shiga gidan gunkinsa, sai waɗansu daga cikin 'ya'yan cikinsa suka kashe shi da takobi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin ’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Tarihi 32:21
34 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

An kwashe ganimar sojojinsu masu ƙarfin hali, Yanzu suna barci, barcin matattu, Ba waninsu da ya ragu, Da zai yi amfani da makamansa.


Nan take sai mala'ikan Ubangiji ya buge shi don bai ɗaukaka Allah ba. Sai tsutsotsi suka yi ta cinsa har ya mutu.


Allahna ya aiko mala'ikansa ya rufe bakunan zakoki, ba su iya yi mini lahani ba, domin ban yi wa Allah laifi ba, ban kuma yi maka ba.”


“Ni kaɗai ne Ubangiji Allahnka. Ba wani allahn da zai sami ɗaukakata, Ba zan bar gumaka su sami yabona ba.


Sa'an nan Ishaya ya aiki manzo zuwa wurin sarki Hezekiya, ya faɗa masa amsar Ubangiji a kan addu'ar sarki.


Ba ka yi daidai da ka ƙi ko wani marar maƙami a shugabannin Assuriya ba, duk da haka kana sa rai ga Masarawa su aiko maka da karusai, da mahayan dawakai!


Ya yi kurari, ya ce, “Kowane shugaban mayaƙana sarki ne!


Girmankai jagora ne zuwa ga hallaka, fāriya kuwa zuwa ga fāɗuwa.


Masu girmankai za a kunyatar da su nan da nan. Hikima ce mutum ya zama mai kamewa.


Zan sa maƙiyansa su sha kunya, Amma mulkinsa zai arzuta. Ya kuma kahu.”


Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai, Ya tsoratar da manyan sarakuna.


Amma mutane suna jin tsoronka! Wa zai iya tsayawa a gabanka Sa'ad da ka yi fushi?


Kullayaumi Allah yakan ba sarkin da ya naɗa babbar nasara. Yakan nuna madawwamiyar ƙauna ga wanda ya zaɓa, Wato Dawuda da zuriyarsa har abada.


Allah mai hikima ne, mai iko, Ba wanda zai iya ja in ja da shi.


Sa'an nan Ishaya, ɗan Amoz, ya aika wa Hezekiya cewa, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ji addu'arka, ya kuma amsa.”


Sa'ad da mala'ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima don ya hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala'ikan da yake hallakar da mutanen, “Ya isa, ka janye hannunka.” Mala'ikan ya tsaya kusa da masussukar Arauna Bayebuse.


Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allah na Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, wanda ya aiko da mala'ikansa, ya ceci bayinsa masu dogara gare shi, waɗanda kuma ba su yarda su bi umarnin sarki ba, amma suka gwammace a ƙone su maimakon su bauta wa gunki, ko su yi masa sujada, sai dai ga Allahnsu kaɗai.


Sai sarki Hezekiya, da annabi Ishaya ɗan Amoz, suka yi addu'a saboda wannan al'amari, suka yi kuka zuwa Sama.


Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mazaunan Urushalima daga hannun Sennakerib Sarkin Assuriya, daga kuma hannun dukan maƙiyansa, ya hutar da su ta kowace fuska.


Kullum a cikin kunya nake, Kunya ta lulluɓe ni ɗungum,


Sa'ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu, Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu.


Zan hallaka Assuriyawa a ƙasata ta Isra'ila, in tattake su a kan duwatsuna. Zan 'yantar da jama'ata daga karkiyar Assuriyawa, daga nauyin da suka tilasta musu su ɗauka.


“Ka tambayar mana Ubangiji, gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kawo mana yaƙi. Ko Ubangiji zai yi mana al'amuran nan nasa masu ban al'ajabi kamar yadda ya saba, ya sa Sarkin Babila ya janye, ya rabu da mu?”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ