Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Tarihi 21:20 - Littafi Mai Tsarki

20 Yana da shekara talatin da biyu, ya ci sarauta, ya yi shekara takwas yana mulki a Urushalima, ba wanda ya yi baƙin cikin mutuwarsa. Aka binne shi a birnin Dawuda, amma ba a kaburburan sarakuna ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Tarihi 21:20
11 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, “Ba za su yi makoki dominsa ba, ko su ce, ‘Wayyo ɗan'uwanmu!’ ko, ‘Wayyo 'yar'uwarmu!’ Ba za su yi makoki dominsa ba, su ce, ‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’


Ashe, Yekoniya kamar fasasshen tulu yake, Wanda ba wanda ya kula da shi? Me ya sa aka watsar da shi da 'ya'yansa, A ƙasar da ba su sani ba?


Ahaz ya rasu, suka binne shi cikin birnin Urushalima, amma ba su kai shi hurumin sarakunan Isra'ila ba. Hezekiya ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.


Sa'ad da suka tafi, sun bar shi da rauni mai tsanani ƙwarai, sai barorinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a gadonsa, saboda ya kashe ɗan Yehoyada firist. Ya mutu, aka binne shi a birnin Dawuda, amma ba su binne shi a kabarin sarakuna ba.


Tunawa da mutumin kirki albarka ce, amma nan da nan za a manta da mugaye.


Dukan jama'ar ƙasar suka yi murna, zaman lafiya ya komo birnin, bayan da an kashe Ataliya.


Yoram kuwa ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Ahaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.


Suka binne shi a birnin Dawuda a inda ake binne sarakuna, saboda ya aikata nagarta a Isra'ila, da kuma a gaban Allah da Haikalin Allah.


Azariya ya rasu, suka binne shi tare da kakanninsa a hurumin sarakuna, gama suka ce, “Shi kuturu ne.” Sai Yotam ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.


Sauran ayyukansa da dukan al'amuransa, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuza da na Isra'ila.


Haka fa Manassa ya rasu, suka binne shi a gidansa, sai Amon ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ