Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Sarakuna 21:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji, gama ya aikata abubuwa masu banƙyama waɗanda al'umman da Ubangiji ya kora a gaban jama'ar Isra'ila suka aikata.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Sarakuna 21:2
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Samariya ba ta aikata rabin zunubin da kika aikata ba. Abubuwan banƙyama da kika aikata sun sa 'yan'uwanki sun zama kamar adalai.


Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, Sarkin Yahuza ya aikata a Urushalima.


Dukan manyan firistoci da sauran jama'a gaba ɗaya, sun zama marasa aminci ƙwarai suna aikata dukan abubuwan banƙyama da al'ummai suke yi. Suka ƙazantar da Haikalin Ubangiji wanda ya tsarkake a Urushalima.


domin sun rabu da ni, sun ƙona turare ga gumaka don su tsokane ni in yi fushi da aikin hannuwansu. Saboda haka fushina zai ƙuna a kan wurin nan, ba kuwa zai huce ba.’


Banda wannan kuma Manassa ya kashe adalai har ya cika Urushalima daga wannan gefe zuwa wancan da jininsu, banda zunubin da ya sa mutanen Yahuza su yi, har suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji.


Siffar gunkiyan nan Ashtoret wadda ya yi, ya kafa ta a Haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Sulemanu, “A cikin wannan Haikali a Urushalima wadda na zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra'ila zan tabbatar da sunana har abada.


Kada ku yi wa Ubangiji Allahnku haka, gama sun yi wa gumakansu dukan abar ƙyamar da Ubangiji yake ƙi, har sun ƙona wa gumakansu 'ya'yansu mata da maza.


“Tun da yake Manassa, Sarkin Yahuza, ya aikata waɗannan abubuwa masu banƙyama, ya kuma aikata mugayen abubuwa fiye da dukan abin da Amoriyawa, waɗanda suka riga shi, suka aikata, ya kuma sa mutanen Yahuza su yi zunubi saboda gumakansa,


Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa, Manassa ya yi.


Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda kakanninsa suka yi.


Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa ya yi.


Hikima ta fi makaman yaƙi, amma mai zunubi ɗaya yakan yi ɓarna mai yawa.


Saboda haka zan aukar musu da masifa, ainihin abin da suke jin tsoro, gama ba wanda ya amsa sa'ad da na yi kira, ko ya kasa kunne sa'ad da na yi magana. Suka zaɓa su yi mini rashin biyayya, su kuma aikata mugunta.”


Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar sauran sarakunan Isra'ila da suka riga shi ba.


Ya bi halin tsohonsa duka. Ya bauta wa gumakan da tsohonsa ya bauta wa, ya kuma yi musu sujada.


Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji, gama ba ku kiyaye dokokina da ka'idodina ba, amma kuka kiyaye ka'idodin sauran al'umma waɗanda suke kewaye da ku.’ ”


Sai ka ce masa, ‘Ni Ubangiji Allah na ce, birnin da yake kisankai, yana kuma bauta wa gumaka don ya ƙazantar da kansa, lokacinsa zai yi!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ