Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 22:48 - Littafi Mai Tsarki

48 Ya ba ni nasara a kan abokan gabana, Ya sa mutane a ƙarƙashin mulkina,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 22:48
11 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Shi yake kiyaye ni, Shi yake kāre ni, Shi ne mafakata da Mai Cetona, Wanda nake dogara gare shi Don samun zaman lafiya. Shi ne ya ɗora ni a kan al'ummai.


Ya Ubangiji, kai Allah ne wanda yake yin hukunci, Ka bayyana fushinka!


Domin kuwa lalle ne ya yi mulki, har ya take dukkan maƙiyansa.


Ubangiji ya ce wa Mai Girma, Sarkina, “Zauna nan a damana, Har in sa maƙiyanka a ƙarƙashin sawayenka.”


Sai ga Bahabashe ya iso, ya ce, “Abishirinka, ya ubangijina, sarki, gama a wannan rana ta yau Ubangiji ya cece ka daga hannun waɗanda suka tayar maka.”


Ahimawaz ɗan Zadok ya ce wa Yowab, “Ka yarda mini in sheƙa a guje in kai wa sarki labari yadda Ubangiji ya cece shi daga hannun magabtansa.”


Sa'ad da Dawuda ya ji Nabal ya mutu, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya sāka mini a kan irin rainin da Nabal ya yi mini. Ya kuma hana ni aikata mugunta. Ya ɗora wa Nabal muguntarsa a kansa.” Sa'an nan Dawuda ya aika, ya nemi Abigail ta zama matarsa.


Sa'ad da Ubangiji ya cika maka dukan alherin da ya yi maka alkawari, ya kuma naɗa ka Sarkin Isra'ila,


Ubangiji dai zai shara'anta tsakanina da kai, ya sāke mini, amma hannuna ba zai taɓa ka ba.


Suka kai wa Dawuda kan Ish-boshet a Hebron. Suka ce wa sarki Dawuda, “Ga kan Ish-boshet ɗan maƙiyinka, Saul, wanda ya nemi ranka. Ubangiji ya rama wa sarki a kan Saul da zuriyarsa yau.”


Sakayya da ɗaukar fansa nawa ne, A lokacin ƙafarsu za ta zame, Gama ranar masifarsu ta kusa, Hallakarsu za ta zo da sauri.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ