Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 22:31 - Littafi Mai Tsarki

31 “Allahn nan cikakke ne ƙwarai, Maganarsa tabbatacciya ce! Kamar garkuwa yake Ga dukan masu neman kiyayewarsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 22:31
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Shi Dutse ne, aikinsa kuma cikakke ne, Gama dukan hanyoyinsa masu adalci ne. Allah mai aminci ne, babu rashin gaskiya a gare shi, Shi mai adalci ne, nagari ne kuma.


“Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa.


Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai, Maganarsa abar dogara ce! Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.


Saboda haka sai ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na Sama take cikakke.”


Alkawarinka ba ya tashi! Bawanka yana ƙaunar alkawarinka ƙwarai!


Alkawaran Ubangiji abin dogara ne, Alkawarai ne na ainihi kamar azurfa Da aka tace har sau bakwai cikin matoya.


Allahna, shi ne kāriyata, Ina zaune lafiya tare da shi. Yana kāre ni kamar garkuwa, Yana tsare ni, ya kiyaye ni. Shi ne mai cetona.


Ɗauki garkuwa da makamanka, ka zo ka taimake ni.


Zai rufe ka da fikafikansa, Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu. Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.


Duba, ya Allah, kai ne garkuwarmu, Ka dubi fuskar Sarkinmu, zaɓaɓɓenka.


Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa, “Ayyukanka manya ne, masu banmamaki, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki! Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma, Ya Sarkin al'ummai.


Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin Samaniya, ina ɗaukaka shi, ina kuma girmama shi saboda dukan ayyukansa daidai ne, al'amuransa kuma gaskiya ne. Yakan ƙasƙantar da masu girmankai.”


Sarkin ya ce, “Zan yi shelar abin da Ubangiji ya hurta. Ubangiji ya ce mini, ‘Kai ɗana ne, Yau ne na zama mahaifinka.


Ka iske shi amintacce a gare ka, Ka kuwa yi masa alkawari. Ka yi alkawari za ka ba shi ƙasar Kan'ana, Da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, Da ta Yebusiyawa, da ta Girgashiyawa, Ta zama inda zuriyarsa za su zauna. Ka kuwa cika alkawarinka, gama kai mai aminci ne.


“Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai, Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne, A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure,


Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka, Mai jinƙai ne a ayyukansa duka.


Na sani dukan abin da Allah ya yi zai dawwama, ba abin da za a ƙara, ko a rage. Allah ya yi haka kuwa domin mutane su zama masu tsoronsa.


“A ƙarshen kwanakin, sai ni Nebukadnezzar, na ɗaga ido sama, sai hankalina ya komo mini, na ɗaukaka Maɗaukaki, na yabe shi, na girmama shi wanda yake rayayye har abada. “Gama mulkinsa madawwamin mulki ne, Sarautarsa kuwa daga zamani zuwa zamani.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ