Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 21:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Ana nan sai Filistiyawa suka kai wa Isra'ilawa yaƙi. Dawuda kuwa ya gangara tare da jama'arsa, suka yi yaƙi da Filistiyawa. Dawuda kuwa ya gaji.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 21:15
14 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

A lokacin nan hannuwanka da suke kāre ka, za su yi makyarkyata, ƙafafunka za su rasa ƙarfi. Haƙora kaɗan za su ragu a bakinka. Idanunka za su duhunta.


Yanzu da na tsufa, kada ka yashe ni, Yanzu da ƙarfina ya ƙare kuma, kada ka rabu da ni!


Bayan wannan kuma, sai yaƙi ya tashi a Gat tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa, sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar ƙattin nan. Aka ci Filistiyawa.


Sai Dawuda ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya yi ta bugun Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.


Filistiyawa suka sāke haurawa, suka bazu a kwarin Refayawa.


Sa'ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila, sai dukansu suka haura zuwa neman ran Dawuda. Da Dawuda ya ji Filistiyawa suna nemansa, sai ya gangara zuwa kagara.


Kwanyata da jikina za su raunana, Amma Allah ne ƙarfina, Shi nake so har abada!


Yanzu da na tsufa, na kuma yi furfura, Kada ka rabu da ni, ya Allah! Ka kasance tare da ni sa'ad da nake shelar ikonka da ƙarfinka ga mutanen dukan zamanai masu zuwa.


Sai Ishbi-benob, ɗaya daga cikin Refayawa, gwarzayen nan, wanda nauyin mashinsa ya yi shekel ɗari uku na tagulla, yana kuma rataye da sabon takobi, ya zaci zai iya kashe Dawuda.


Bayan haka kuma sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ