Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 19:29 - Littafi Mai Tsarki

29 Sai sarki ya ce masa, “Me ya kawo wannan magana a kan harkokinka? Ai, na riga na zartar, cewa, kai da Ziba za ku raba mallakar Saul.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

29 Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 19:29
11 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Amma tun da yake gardama ce kawai a kan kalmomi, da sunaye, da kuma shari'arku, ai, sai ku ji da ita, ku da kanku. Ni kam, ba ni da niyyar yin shari'a irin waɗannan abubuwa.”


Ka saurara kafin ka amsa, idan kuwa ba ka yi ba, ka zama dakiki mai bankunya.


Zan hallakar da mai raɗar abokinsa, Ba zan jure da mutum mai girmankai, Ko mai alfarma ba.


Tilas ku daina yin rashin gaskiya a shari'a, Ku daina goyon bayan mugaye!


Akwai wani bara na gidan Saul, sunansa Ziba. Sai aka kirawo shi wurin sarki Dawuda. Sarki ya tambaye shi, “Kai ne Ziba?” Sai ya amsa, “Ranka ya daɗe, ni ne.”


Sa'an nan sarki ya kira Ziba, baran Saul, ya ce masa, “Dukan abin da yake na Saul, da dukan abin da yake na iyalinsa, na ba ɗan maigidanka.


Gama dukan mutanen gidan kakana sun cancanci mutuwa a gabanka, ranka ya daɗe, amma ga shi, ka sa na zama ɗaya daga cikin waɗanda suke ci a teburinka. Ba ni da dalilin da zai sa in yi wa sarki wani kuka kuma.”


Mefiboshet ya ce wa sarki, “A ma bar masa duka ya mallaka, ni dai tun da ubangijina, sarki, ya komo gida lafiya, to, alhamdu lillahi.”


Dawuda ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, gama zan yi maka alheri ne saboda mahaifinka, Jonatan. Zan mayar maka da dukan gonakin kakanka, Saul. Kullum kuma za ka riƙa cin abinci a teburina.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ