Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 1:21 - Littafi Mai Tsarki

21 “Kada ruwan sama ko raɓa su zubo kan tuddan Gilbowa. Da ma gonakinta su zama marasa ba da amfani. Gama a can ne aka zube garkuwoyin jarumawa a wulakance, Tsatsa ta rufe garkuwar Saul.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 1:21
14 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa. Isra'ilawa kuma suka yi gudun Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa.


A wahayin na ga an shirya biki, an shisshimfiɗa darduma inda waɗanda aka gayyata za su zauna. Suna ci suna sha. Farat ɗaya sai aka ji umarni cewa, “Jarumawa! Ku shirya garkuwoyinku.”


Sa'an nan Sama'ila ya ɗauki 'yar kwalabar mai, ya zuba wa Saul a kā, ya yi masa sumba, ya ce, “Ubangjiji ne ya keɓe ka, ya naɗa ka sarki a kan jama'arsa.


Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zai sāke nufinsa, Ya sa mana albarka, Har mu miƙa masa hadaya ta gari da ta sha?


Ba hatsi ko ruwan inabin Da za a yi hadaya da su cikin Haikalin. Firistoci masu miƙa wa Ubangiji hadaya suna makoki.


Ubangiji Allah ya ce, “A ranar da ya gangara zuwa lahira, na sa zurfi ya rufe shi, ya yi makoki dominsa. Na tsai da kogunansa, yawan ruwansa ya ƙafe. Na sa Lebanon ta yi duhu saboda shi. Dukan itatuwan jeji kuwa sun yi yaushi saboda shi.


Zan bar ciyayi su rufe ta. Ba zan yi wa kurangar inabin aski ba, ko in yi mata noma, amma zan bar sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa su rufe ta. Har ma zan sa gizagizai su hana ta ruwan sama.”


Kashegari, sa'ad da Filistiyawa suka tafi su kwashe waɗanda aka kashe, sai suka tarar da Saul da 'ya'yansa maza matattu a Dutsen Gilbowa.


Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa, Isra'ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa.


Mala'ikan Ubangiji ya ce, “Ka la'anta Meroz, Ka la'anta mazauna cikinta sosai, Gama ba su kawo wa Ubangiji gudunmawa ba, Su zo su yi yaƙi kamar sojoji dominsa.”


Wuyanki kamar hasumiyar Dawuda yake, kewayayye sumul sumul, Inda aka rataye garkuwoyi dubu na jarumawa.


Da Filistiyawa suka zo kashegari don su washe kayan kisassun, sai suka tarar da gawar Saul da gawawwakin 'ya'yansa uku a kan Dutsen Gilbowa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ