Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Korintiyawa 7:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Ku dubi fa irin himmar da baƙin cikin nan, da Allah yake so ya sa a zukatanku, da irin ɗokin da kuka yi na gyara al'amuranku, da irin haushin da kuka ji, da irin tsoron da kuka ji, da irin begen da kuka yi, da irin himmar da kuka yi, da kuma irin niyyarku ta horo. A game da wannan sha'ani kam, lalle ta kowace hanya kun nuna cewa ba ku da laifi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 Ku dubi abin da wannan baƙin ciki irin na tsoron Allah ya kawo muku mana, ya sa ku marmarin aikatawa, da nuna cewa kun yi kuskure, ya sa kuka yi fushi, kuka kuma ji tsoro, ya sa kuka sa zuciya, kuka kuma sa aniya, ya sa kuna a shirye ku ga an yi horon da ya dace. Game da wannan sha’ani kam, lalle ta kowace hanya kun nuna cewa ba ku da laifi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Korintiyawa 7:11
54 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Wanda duk yake bauta wa Almasihu ta haka, abin karɓa ne ga Allah, yardajje ne kuma ga mutane.


Ka himmantu, ka miƙa kanka yardajje ga Allah, ma'aikaci wanda ba hanya ya kunyata, mai kuma fassara Maganar gaskiya daidai.


ba kuwa da zuwan Titus kawai ba, har ma a game da ƙarfafa zuciyar nan da ya samu a wurinku, a yayin da ya gaya mana yadda kuke begena, kuna nadama, kuna kuma himmantuwa ga goyan bayana, har ma na ƙara farin ciki ƙwarai.


Allah ne yake hukunta waɗanda ba namu ba. Ku kori mugun nan daga cikinku.


Ku bauta wa Ubangiji da tsoro, Ku yi rawar jiki, ku rusuna masa,


Waɗanda nake ƙauna, su nake tsawata wa, nake kuma horo. Saboda haka, sai ka himmantu ka tuba.


kuna ceton waɗansu kuna fizgo su daga wuta. Waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro kuna ƙyamar ko da tufafin da halinsu na mutuntaka ya ƙazantar.


Kamar jariri sabon haihuwa, ku yi marmarin shan madara marar gami mai ruhu, domin ku girma da shi, har ya kai ku ga samun ceto,


Da yake kuna kiransa Uba a wajen addu'a, shi da yake yi wa kowa shari'a gwargwadon aikinsa, ba zaɓe, sai ku ƙarasa lokacin baƙuncinku, kuna tsoronsa.


Saboda haka tun alkawarin shiga inuwarsa tana nan, sai mu yi tsananin kula, kada ya zamana waninku ya kāsa shiga.


Maganar nan tabbatacciya ce. Ina so ka ƙarfafa waɗannan abubuwa ƙwarai, don waɗanda suka ba da gaskiya ga Allah su himmantu ga aiki nagari, waɗannan abubuwa kuwa masu kyau ne, masu amfani kuma ga mutane.


Saboda haka, ya ƙaunatattuna, kamar yadda a kullum kuke biyayya, haka kuma yanzu, ku yi ta yin aikin ceton nan naku da halin bangirma tare da matsananciyar kula, ba ma sai ina nan kawai ba, har ma fiye da haka in ba na nan.


Ku yi nesa da ayyukan duhu na banza da wofi, sai dai ku tona su.


In kun husata, kada ku yi zunubi, kada ma fushinku ya kai faɗuwar rana,


Amma muna roƙon Allah kada ku yi wani mugun abu, ba don mu mu zama kamar mun ci gwajin kawai ba, sai dai domin ku yi abin da yake daidai, ko da yake za ku ga kamar mun kāsa.


domin na san niyyarku, har ma ina taƙama da ku gun mutanen Makidoniya a kan haka, ina ce musu Ikkilisiyar Akaya ta yi shiri tun bara, ƙwazonku kuwa ya ta da yawancinsu.


Ya ku ƙaunatattu, tun da aka yi mana waɗannan alkawarai, sai mu tsarkake kanmu daga kowace irin ƙazanta ta jiki ko ta zuci, da bangirma ga Allah mu kamalta a cikin tsarki.


Amma ta kowace hanya muna bayyana gaskiyarmu, a kan bayin Allah muke, ta matuƙar jurewa, da shan wahala, da ƙuntata, da masifu,


Irin mutumin nan, horon nan da galibin jama'a suka yi masa, ai, ya isa haka.


kada rashin haɗa kai ya kasance ga jiki, sai dai gaɓoɓin su kula da juna, kula iri ɗaya.


A! Har kuwa alfarma kuke yi! Ashe, ba gwamma ku yi baƙin ciki ba, har a fitar da wanda ya yi wannan mugun aiki daga cikin jama'arku?


Hakika haka ne, amma saboda rashin bangaskiyarsu ne aka sare su, kai kuwa saboda bangaskiyarka ne kake kafe. Kada fa ka nuna alfarma, sai dai ka ji tsoron Allah.


To, sa'ad da Bulus yake dākonsu a Atina, ya ji haushi ƙwarai da ya ga ko'ina gumaka ne a birnin.


Sai almajiransa suka tuna a rubuce yake cewa, “Kishin Haikalinka ya ci raina matuƙa.”


Da ya duddube su da fushi, yana baƙin ciki da taurin zuciyarsu, sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.


Sa'ad da sarki ya ji wannan magana, sai ransa ya ɓaci ƙwarai, sai ya shiga tunani ta yadda zai yi ya kuɓutar da Daniyel. Ya yi ta fama har faɗuwar rana yadda zai yi ya kuɓutar da shi.


Ni kaina na halicci dukan kome ka kome! Ina jin daɗin waɗanda suke da tawali'u, da kuma masu tuba, waɗanda suke tsorona suna kuwa biyayya gare ni.


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


Kada ki ƙaunaci kowa sai ni, Kada ki rungume kowa sai ni. Ikon ƙauna kamar na mutuwa ne, Ƙarfin kishin ƙauna kamar na mutuwa ne. Yakan kama kamar wuta, Yakan ci kamar gagarumar wuta.


Mutumin da yake tsoron Ubangiji ko yaushe, zai yi farin ciki, amma idan ya taurare zai lalace.


Mutum mai hankali yana lura don ya kauce wa wahala, amma wawa rashin kula gare shi, yakan aikata kome da gaggawa.


Yakan biya bukatar dukan waɗanda suke tsoronsa, Yakan ji kukansu, ya cece su.


Ina jiran Ubangiji, Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir, I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir.


Fushi yana cina kamar wuta, Saboda maƙiyana ba su kula da umarnanka ba.


Ƙaunar da nake da ita ta yin ibada a Haikalinka Tana iza ni a ciki kamar wuta, Zargin da suke yi a kanka, ya fāɗa a kaina.


Kamar yadda kishimi yake marmarin ruwan sanyi daga rafi, Haka nake marmarinka, ya Allah.


Ka san bukatata, ya Ubangiji, Kana jin dukan nishe-nishena.


Amma sa'ad da suke ciwo, nakan sa tufafin makoki, Na ƙi cin abinci, Na yi addu'a da kaina a sunkuye,


Sai na yi musu faɗa na la'ance su, na bugi waɗansu daga cikinsu, na ciccire gashin kansu, na sa su rantse da Allah, cewa ba za su aurar da 'ya'yansu mata ga 'ya'yan maza na bare ba, ko kuma su auro wa 'ya'yansu maza 'yan matan bare, ko su auro wa kansu.


Amma a yanzu kam, ina farin ciki, ba don kun yi baƙin ciki ba, sai dai don baƙin cikinmu ya sa ku tuba, don kun yi baƙin ciki irin wanda Allah yake so. Saboda haka, ba ku yi hasarar kome a sanadinmu ba.


Saboda haka na ga ni ba kome ba ne, Na tuba, ina hurwa da ƙura da toka.”


In kuwa rashin adalcinmu shi ne yake nuna adalcin Allah a fili, me za mu ce? in Allah ya hore mu, ya yi rashin adalci ke nan? (Misali nake yi kawai.)


A cikin wannan al'amari kuwa kada kowa ya keta haddi, har ya cuci ɗan'uwansa, domin Ubangiji mai sakamako ne a kan dukkan waɗannan abubuwa, kamar yadda muka gargaɗe ku, muka tabbatar muku tun da wuri.


Masu yin zunubi kuwa, sai ka tsawata musu a gaban dukkan jama'a, don saura su tsorata.


Amma hikimar nan ta Sama, da farko dai tsattsarka ce, mai lumana ce, saliha ce, mai sauƙin kai, mai tsananin jinƙai, mai yawan alheri, mai kaifi ɗaya, sahihiya kuma.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ