Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




1 Tarihi 24:5 - Littafi Mai Tsarki

5 Da haka aka karkasa su ta hanyar kuri'a gama akwai ma'aikatan Wuri Mai Tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Ele'azara da zuriyar Itamar.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




1 Tarihi 24:5
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Su ma suka jefa kuri'a kamar yadda 'yan'uwansu, 'ya'yan Haruna, maza, suka yi a gaban sarki Dawuda, da Zadok, da Ahimelek, da shugabannin gidajen kakanni na firistoci da na Lawiyawa. Shugaban gidan kakanni ya jefa kuri'a daidai da ƙanensa.


To, da shugaban dogaran Haikali da manyan firistocin suka ji haka, suka ruɗe ƙwarai a game da su, suka rasa inda abin zai kai.


tare da Hanana, babban firist, da Kayafa, da Yahaya, da Iskandari, da kuma duk waɗanda suke dangin babban firist.


Suna cikin yin magana da jama'a sai firistoci da shugaban dogaran Haikali da Sadukiyawa suka ji haushi ƙwarai, suka aukar musu,


Sai suka yi musu kuri'a, Matiyas ya ci, aka kuma sa shi a cikin manzannin nan goma sha ɗaya.


Da gari ya waye sai duk manyan firistoci da shugabannin jama'a suka yi shawara a kan Yesu su kashe shi.


Sai manyan firistoci da shugabannin jama'a suka taru a gidan babban firist, mai suna Kayafa.


Matuƙan jirgin kuwa suka ce wa junansu, “To, bari mu jefa kuri'a mu gani ko alhakin wane ne ya jawo mana wannan bala'i da muke ciki.” Sai suka jefa kuri'a, kuri'ar kuwa ta fāɗa a kan Yunusa.


Mutane sukan jefa kuri'a don su san nufin Allah, amma Allah da kansa ne yake ba da amsa.


da Seraiya ɗan Hilkiya, jīkan Shallum. Sauran kakanninsa, su ne Zadok, da Merayot, da Ahitub, mai lura da Haikalin Allah.


Da yardar rai manyan ma'aikatansa, sarakunansa, suka ba da gudunmawa ga jama'ar, da firistoci, da Lawiyawa. Hilkiya, da Zakariya, da Yehiyel, manyan ma'aikatan Haikalin Allah, suka ba firistoci abin yin hadaya don Idin Ƙetarewa, tumaki da awaki dubu biyu da ɗari shida (2,600), da bijimai ɗari uku.


da Azariya ɗan Hilkiya, shi ne jami'in Haikalin Ubangiji, kakanninsa sun haɗu da Shallum ɗan Zadok, da Merayot, da Ahitub,


Joshuwa kuwa ya jefa musu kuri'a a gaban Ubangiji a Shilo. Ta haka ya rarraba ƙasar ga jama'ar Isra'ila, kowa ya sami rabonsa.


Tun da yake akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Ele'azara fiye da zuriyar Itamar, sai suka karkasa su haka, shugabannin gidajen kakannin zuriyar Ele'azara mutum goma sha shida, na zuriyar Itamar kuwa su takwas, bisa ga gidajen kakanninsu.


Sai suka jefa kuri'a bisa ga gidajen kakanninsu, ba a damu da yawan jama'a a iyali ba, a kan kowace ƙofar.


Sai suka jefa kuri'a domin su ba kowa aikin da zai yi, yaro da babba, malami da almajiri.


Zan musunci masu mulkin tsattsarkan masujadai, Saboda haka zan jawo wa Isra'ila hallaka, Zan bari a la'anta mutanena su sha zagi!”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ