Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




1 Sarakuna 8:36 - Littafi Mai Tsarki

36 sai ka ji daga Sama, ka gafarta zunuban sarki, da na jama'arka Isra'ila. Ka koya musu kyakkyawar hanyar da za su bi, ka sa a yi ruwan sama a ƙasarka wadda ka ba jama'arka gādo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




1 Sarakuna 8:36
28 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ka koya mini abin da ya kamata in yi, ya Ubangiji, Ka bi da ni kan lafiyyiyar hanya, Domin ina da magabta da yawa.


Amma ni kaina, Allah ya sawwaƙa in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin fasa yin addu'a ga Ubangiji dominku. Zan riƙa koya muku kyawawan abubuwan da suke daidai.


Haka Ubangiji ya ce, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba, Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya mai kyau take, Ku bi ta, don ku hutar da rayukanku. Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’


A cikin gumakan al'ummai akwai mai iya sa a yi ruwa? Sammai kuma su yi yayyafi? Ashe, ba kai ne ba, ya Ubangiji Allahnmu? Domin haka a gare ka muke sa zuciya, Gama kai ne mai yin waɗannan abubuwa duka.”


Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa, Mutumin da kake koya masa shari'arka.


Jim kaɗan sai sararin sama ya yi baƙi ƙirin da gizagizai da iska, aka yi ruwan sama mai yawan gaske. Ahab kuwa ya hau karusarsa ya tafi Yezreyel.


Bayan 'yan kwanaki, sai Ubangiji ya yi magana da Iliya a shekara ta uku, ya ce, “Tafi, ka nuna kanka ga Ahab, ni kuwa zan sa a yi ruwan sama.”


Suka aiko almajiransu wurinsa tare da waɗansu mutanen Hirudus, suka ce, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi, ba ka kuma zaɓen kowa, don ka ɗauki kowa da kowa daidai.


Al'umman duniya za su zo, su ce, “Bari mu haura zuwa tudun Ubangiji, Zuwa Haikalin Allah na Isra'ila, Za mu koyi abin da yake so mu yi, Za mu yi tafiya a hanyar da ya zaɓa.” Koyarwar Ubangiji daga Urushalima take zuwa, Daga Sihiyona yake magana da jama'arsa.


Ka yi mana addu'a domin Ubangiji Allahnka ya nuna mana hanyar da za mu bi, da kuma abin da za mu yi.”


Za a yi babbar karauka a can, Za a kira ta, “Hanyar Tsarki.” Ba mai zunubi da zai taɓa bi ta wannan hanya, Ba wawayen da za su ruɗar da waɗanda suke tafiya can.


Idan kuka kauce daga hanya zuwa dama ko hagu, za ku ji muryarsa a bayanku yana cewa, “Ga hanyan nan, ku bi ta.”


A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi.


Ka koya mini ma'anar dokokinka, ya Ubangiji, Zan kuwa yi biyayya da su a kowane lokaci.


Ya Ubangiji, ka koya mini abin da kake so in yi, Ni kuwa zan yi maka biyayya da aminci. Ka koya mini in bauta maka da zuciya ɗaya.


Ka sa aka yi ruwan sama mai yawa, ya Allah, Ka rayar da ƙasarka wadda ta zozaye.


Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi, Zan koya maka, in kuma ba ka shawara.


Waɗanda suke biyayya da Ubangiji Za su koyi hanyar da za su bi daga gare shi.


Ubangiji mai adalci ne, mai alheri, Yana koya wa masu zunubi tafarkin da za su bi.


Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji, Ka bi da ni in aikata nufinka, Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta!


Iliya kuwa ya ce wa Ahab, “Sai ka haura ka ci ka sha, gama akwai motsin sakowar ruwan sama.”


Kada ka bar ni in fāɗi kamar yadda ka alkawarta, Kada ka bar mugunta ta rinjaye ni.


Jama'arka suka gina gidajensu a can, Ta wurin alherinka ka yi wa matalauta tanadi.


Ya ku mutanen Sihiyona, ku yi murna, Ku yi farin ciki da Ubangiji Allahnku, Gama ya ba ku ruwan farko Domin shaidar gafarar da ya yi muku, Ya kwararo muku da ruwan farko da na ƙarshe da yawa kamar dā.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ