Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




1 Sarakuna 5:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Da Hiram ya ji maganar Sulemanu, sai ya yi murna ƙwarai, ya ce, “Yabo ga Ubangiji saboda wannan rana, gama ya ba Dawuda ɗa mai hikima da zai shugabanci wannan babbar jama'a.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




1 Sarakuna 5:7
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ga shi, an haifa mana ɗa! Mun sami yaro! Shi zai zama Mai Mulkinmu. Za a kira shi, “Mashawarci Mai Al'ajabi,” “Allah Maɗaukaki,” “Uba Madawwami,” “Sarkin Salama.”


Mahaifin adali yana da dalilin yin murna. Zai yi fāriya a kan ɗa mai hikima.


Ga ni tare da 'ya'yan da Ubangiji ya ba ni. Ubangiji Mai Runduna, wanda kursiyinsa a kan Dutsen Sihiyona yake, ya maishe mu rayayyen jawabi ga jama'ar Isra'ila.


Ɗa mai hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa, amma wawa yana raina mahaifiyarsa.


Ɗa mai hikima yakan mai da hankali sa'ad da mahaifinsa yake kwaɓarsa, amma mutum mai girmankai ba ya yarda da kuskurensa.


Karin maganar Sulemanu ke nan. Ɗa mai hikima abin fāriya ne ga mahaifinsa, amma wawa yakan jawo wa mahaifiyarsa baƙin ciki.


Da ma kada in ƙara iya raira waƙa, Idan na manta da ke, Idan ban tuna ke ce Babbar abar farin ciki ba!


Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka wanda ya yarda da kai, ya sa ka a kan gadon sarautar Isra'ila, domin Ubangiji yana ƙaunar Isra'ila har abada, ya naɗa ka sarki domin ka zartar da shari'a da adalci.”


Domin haka ka ba ni hikima ta yi wa jama'arka shari'a, domin in rarrabe tsakanin nagarta da mugunta, gama wane ni in iya mallakar jama'arka mai yawa haka?”


Sa'an nan ya ce, ‘Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na Isra'ila wanda ya sa ɗaya daga cikin zuriyata ya hau gadon sarautata yau, idona kuwa ya gani.’ ”


Sa'ad da Isuwa ya ta da idonsa ya ga mata da 'ya'ya, ya ce, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yakubu ya ce, “Su ne 'ya'ya waɗanda Allah cikin alherinsa ya ba baranka.”


Saboda haka sai ka sa a saro mini itatuwan al'ul na Lebanon. Barorina za su haɗu da barorinka, ni kuwa zan biya ka aikin da barorinka za su yi bisa ga yadda ka ce, gama ka sani ba wani daga cikin mutanena da ya iya saran katako kamar mutanenka.”


Sa'an nan Hiram ya aika wurin Sulemanu, ya ce, “Na ji saƙonka da ka aiko mini, a shirye nake in yi maka dukan abin da kake bukata a kan katakan itacen al'ul, da na fir.


Sulemanu kuma ya naɗa mutum goma sha biyu a lardunan Isra'ila. Su ne za su tanaji abinci daga lardunansu domin sarki da iyalinsa. Kowane hakimi yakan kawo abinci wata guda a shekara.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ