Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




1 Samaʼila 5:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Kashegari da safe sa'ad da mutanen Ashdod suka tashi, sai suka ga Dagon ya faɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Suka ta da shi, suka ajiye a wurinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




1 Samaʼila 5:3
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Wannan shi ne jawabi a kan Masar. Ubangiji yana zuwa Masar a kan girjije a sukwane. Gumakan Masarawa za su yi rawar jiki a gabansa, zuciyar Masarawa za ta karai.


Suka ɗauke shi a kafaɗunsu su tafi da shi, Suna ajiyewa a wani wuri, ya yi ta tsayawa a can, Ba ya iya motsawa daga inda yake. Idan wani ya yi addu'a gare shi, ba zai iya amsawa ba, Ko ya cece shi daga bala'i.


Ubangiji zai tsananta musu, Zai kawo wa dukan gumakan da yake a duniya yunwa. Kowane mutum a duniya zai yi masa sujada a inda yake, Har da ƙasar sauran al'umma.


Baƙaƙen aljannu kuwa, duk sa'ad da suka gan shi, sai su fāɗi gabansa suna kururuwa, suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne.”


Dukansu dakikai ne wawaye, Koyarwar gumaka ba wani abu ba ne, itace ne kawai!


Masassaƙi yakan ce wa maƙerin zinariya, ‘A gaishe ka!’ Wanda yake gyara gumaka ya yi sumul Yana ƙarfafa wanda yake harhaɗa su. Wani yakan ce, ‘Haɗin ya yi kyau,’ Sukan kuma manne gumakan da ƙusoshi.


Mutum wanda bai isa samun azurfa ko zinariya ba, Yakan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yana neman gwanin sassaƙa Domin ya yi masa siffa wadda ba za ta fāɗi ba.


Dukan waɗanda suke yi wa siffofi sujada za su sha kunya, Haka kuma waɗanda suke fāriya da gumakansu. Dukan alloli za su rusuna a gabansa.


A daren nan zan ratsa ƙasar Masar, in bugi kowane ɗan fari na ƙasar, na mutum da na dabba. Zan hukunta gumakan Masar duka, gama ni ne Ubangiji.


Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye waɗanda suka lalatar da ƙasar, ku ba da girma ga Allah na Isra'ila, watakila zai ɗauke hukuncinsa a kanku, da allolinku, da ƙasarku.


Akwatin alkawarin Ubangiji ya yi wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.


Suka kuwa kama bijimin da aka ba su, suka gyara shi suka yi ta kira ga sunan Ba'al tun da safe, har tsakar ranar suna ta cewa, “Ya Ba'al, ka amsa mana!” Amma ba murya, ba kuwa wanda ya amsa. Suka yi ta tsalle a wajen bagaden da suka gina.


Suna da hannuwa, amma ba sa iya riƙon kome, Suna da ƙafafu, amma ba sa iya tafiya. Ba su da murya sam.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ