1 Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
1 Sai Yunusa ya yi addu'a ga Ubangiji Allah a cikin cikin kifin,
Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”
Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo.