Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Obadiya 1:8 - Sabon Rai Don Kowa 2020

8 “A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Littafi Mai Tsarki

8 Ni Ubangiji na ce, “A ranar da zan hukunta Edom, Zan hallaka masu hikimarka, Zan shafe hikima daga dutsen Isuwa.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Obadiya 1:8
8 Iomraidhean Croise  

Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.


Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?


Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.


Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.


Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan