31 Amma suka fita suka yi ta baza labari game da shi ko’ina a wannan yankin.
31 Amma suka tafi suka yi ta baza labarinsa a duk ƙasar.
A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.
Labarin wannan kuwa ya bazu ko’ina a yankin.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi.
Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.