Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Mattiyu 7:24 - Sabon Rai Don Kowa 2020

24 “Saboda haka duk wanda yake jin kalmomin nan nawa yake kuma aikata su, yana kama da mutum mai hikima wanda ya gina gidansa a kan dutse.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Littafi Mai Tsarki

24 “Saboda haka, kowa da yake jin maganar nan tawa, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidansa a kan fā.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Mattiyu 7:24
41 Iomraidhean Croise  

Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’ ”


Tsoron Ubangiji ne mafarin hikima; dukan waɗanda suke bin farillansa suna da ganewa mai kyau. Gare shi ne madawwamin yabo.


Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.


Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.


Sa’ad da hadiri ya taso, yakan watsar da mugaye, amma adalai za su tsaya daram har abada.


Mai hikima a zuciya yakan yarda da umarni amma surutun wawa kan kai ga lalaci.


Akan tumɓuke mugaye ba a ƙara ganinsu, amma gidan masu adalci kan tsaya daram.


Hikima masu la’akari shi ne su yi tunani a kan hanyoyinsu, amma wautar wawaye ruɗu ne.


Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da ’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”


Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hades ba za su rinjaye ta ba.


“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?


Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.


Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.


“Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’


Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuma ta hura ta bugi gidan; duk da haka bai fāɗi ba, gama yana da harsashinsa a kan dutse.


Amma duk wanda yake jin kalmomin nan nawa bai kuwa aikata su ba, yana kama da wani wawa wanda ya gina gidansa a kan yashi.


Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”


Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.


“In kuna ƙaunata za ku yi biyayya da umarnina.


In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.


Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.


Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci.


Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan