Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Mattiyu 27:14 - Sabon Rai Don Kowa 2020

14 Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Littafi Mai Tsarki

14 Amma bai ba shi wata amsa, ko da ta kalma ɗaya ba, har mai mulki ya yi mamaki ƙwarai.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Mattiyu 27:14
10 Iomraidhean Croise  

Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.


Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.


“ ‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.


Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”


Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.


Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”


Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.


Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.


sai ya sāke koma cikin fada. Ya tambayi Yesu, “Daga ina ka fito?” Amma Yesu bai amsa masa ba.


Gama a ganina fa, Allah ya baje mu manzanni a ƙarshen jerin gwanon, a matsayin mutanen da aka hukunta ga mutuwa a filin wasanni. Mun zama abin kallo ga dukan duniya, ga mala’iku da kuma mutane.


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan