Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Mattiyu 25:12 - Sabon Rai Don Kowa 2020

12 “Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Littafi Mai Tsarki

12 Sai ya amsa ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, ni ban san ku ba.’

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Mattiyu 25:12
12 Iomraidhean Croise  

Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.


Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.


Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?


“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’


“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.


Da zaran maigidan ya tashi ya rufe ƙofar, za ku tsaya a waje kuna ƙwanƙwasawa, kuna roƙo cewa, ‘Ranka yă daɗe, buɗe mana ƙofa.’ “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ni ban san ku, ko inda kuka fito ba.’


Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.


Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.


Amma mutumin da yake ƙaunar Allah, Allah yana sane da shi.


Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?


Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan