40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
40 A sa'an nan za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Wa ya ce ka fi sauran mutane? Me kuma kake da shi, wanda ba karɓa ka yi ba? In kuma karɓa ka yi, me ya sa kake taƙama kamar ba karɓa ba ne ka yi?
in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;