33 Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 Da jama'a suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
Da Asabbaci ya kewayo, sai ya fara koyarwa a cikin majami’a, mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki. Suna tambaya, “Ina mutumin nan ya sami waɗannan abubuwa? Wace hikima ce wannan da aka ba shi, har da yana yin ayyukan banmamaki haka!
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”