33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
33 Suka ce masa, “Ya Ubangiji, mu dai mu sami gani!”
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.