Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Ƙidaya 9:8 - Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Littafi Mai Tsarki

8 Sai Musa ya ce musu, “Dakata, har na ji abin da Ubangiji zai umarta a kanku.”

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Ƙidaya 9:8
19 Iomraidhean Croise  

Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’ ”


Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.


Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.


Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.


Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.


Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su ’yan tawaye ne.


“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.


Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.


sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.


Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.


suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”


Sai Ubangiji ya ce wa Musa,


Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.


Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.


Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.


Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,


Lamirina bai ba ni laifi ba, sai dai wannan bai mai da ni marar laifi ba. Ubangiji ne mai hukunta ni.


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan