Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Rut 1:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Daga can Mowab, Na'omi ta ji cewa, Ubangiji ya taimaki mutanensa, ya ba su abinci, sai ta tashi daga ƙasar Mowab tare da surukanta.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Rut 1:6
27 Iomraidhean Croise  

Ubangiji ya yi wa Saratu alheri kamar yadda ya alkawarta.


Yakubu ya yi wa'adi da cewa, “Idan Allah zai kasance tare da ni, ya kiyaye ni cikin tafiyan nan da nake yi, ya kuma ba ni abincin da zan ci, da suturar da zan sa,


Sai ya sa wa Yusufu albarka, ya ce, “Allah na Ibrahim da Ishaku, Iyayena da suka yi tafiyarsu a gabansa, Allah da ya bi da ni Dukan raina har wa yau, ya sa musu albarka.


Sa'an nan Yusufu ya rantse wa 'ya'yan Isra'ila da cewa, “Hakika Allah zai ziyarce ku, ku kuma sai ku haura da ƙasusuwana daga nan.”


Bayinka suna ƙaunarta, Ko da yake an hallakar da ita, Suna jin tausayinta, Ko da yake ta zama kufai.


Yakan tanada wa masu tsoronsa abinci, Bai taɓa mantawa da alkawarinsa ba.


Zan tanada wa Sihiyona dukan abin da take bukata a yalwace, Zan ƙosar da matalautanta da abinci.


Dukan masu rai suna sa zuciya gare shi, Yana ba su abinci a lokacin da suke bukata,


A yanke shari'arsa yakan ba wanda aka zalunta gaskiya. Yana ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan kuɓutar da ɗaurarru.


Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya, Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.


Tafi, ka tattara dattawan Isra'ila, ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah na kakanninku ya bayyana gare ni, wato na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, ya ce, sosai ya ziyarce ku, ya kuma ga abin da ake yi muku a Masar.


Dattawan kuwa suka gaskata. Sa'ad da suka ji Ubangiji ya ziyarci Isra'ilawa, ya kuma ga wahalarsu, sai suka sunkuya, suka yi masa sujada.


Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,


“Maganata kamar dusar ƙanƙara take, Kamar kuma ruwan sama da yake saukowa domin ya jiƙe duniya. Ba za su kasa sa amfanin gona ya yi girma ba, Sukan ba da iri domin shukawa, da abinci kuma domin a ci.


“Ubangiji ya ce, ‘Sa'ad da kuka cika shekara saba'in a Babila, zan ziyarce ku, zan kuwa cika muku alkawarina. Zan komo da ku zuwa wannan wuri.


Sa'an nan ya ce musu, “Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwan inabi, da mai, Za ku ƙoshi. Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi ga al'ummai ba.


Gaɓar teku za ta zama ta mutanen Yahuza waɗanda suka ragu, Wurin da za su yi kiwo. Za su kwanta da maraice a gidajen Ashkelon, Gama Ubangiji Allahnsu zai kula da su, Zai kuwa mayar musu da albarkarsu ta dā.


Ka ba mu abincinmu na yau.


“Ubangiji Allahn Isra'ila, A gare shi ne lalle yabo yake tabbata, Domin ya kula, ya yi wa jama'a tasa fansa.


su fyaɗa ku a ƙasa, ku mutanen birni duka, ba kuma za su bar wani dutse a kan ɗan'uwansa ba a birninku, don ba ku fahimci lokacin da ake sauko muku da alheri ba.”


To, in muna da abinci da sutura, ai, sai mu dangana da su.


Ku yi halin yabo a cikin al'ummai, don duk sa'ad da suke kushenku, cewa ku mugaye ne, sai su ga kyawawan ayyukanku, har su ɗaukaka Allah a ran da alheri ya sauko musu.


sai kuma Malon da Kiliyon suka rasu, Na'omi kuwa ta rasa mijinta da kuma 'ya'yanta maza biyu.


Suka kama hanya zuwa ƙasar Yahudiya.


Ubangiji ya sa wa Hannatu albarka, ta haifi 'ya'ya maza uku da mata biyu. Yaron nan Sama'ila kuwa ya girma a gaban Ubangiji.


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan