Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Mika 1:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Dukanku ku ji, ku al'ummai! Ki kasa kunne, ya duniya, da dukan abin da yake cikinki. Bari Ubangiji Allah Daga Haikalinsa mai tsarki ya zama shaida a kanku.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Mika 1:2
33 Iomraidhean Croise  

Mikaiya kuwa ya ce, “In dai ka komo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana da ni ba.” Ya ƙara da cewa, “Kowa ya kasa kunne ga abin da na faɗa.”


Sai Mikaiya ya ce, “Idan har ka komo lafiya, wato Ubangiji bai yi magana da ni ba ke nan.” Sai ya ce, “Ku ji, ya ku jama'a duka.”


Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Yana da kursiyinsa a Sama. Yana kallon dukan mutane Yana sane da abin da suke yi.


Duniya da dukan abin da yake cikinta na Ubangiji ne, Duniya da dukan mazaunanta nasa ne.


Ka ji ni lokacin da na yi kuka gare ka neman taimako, Ina ɗaga hannuwana wajen tsattsarkan Haikalinka.


Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana, Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma.


“Da ina jin yunwa ba sai na faɗa muku ba, Gama da duniya da dukan abin da yake cikinta nawa ne.


“Ku ji, ya ku jama'ata, zan kuwa yi magana, Zan ba da shaida gāba da ku, ya Isra'ila. Ni ne Allah, Allahnku.


“Ina roƙonku, ya ku, 'yan adam, Ina kiran kowane mutum da yake a duniya.


Ubangiji ya ce, “Duniya da sararin sama, ku kasa kunne ga abin da ni, Ubangiji, nake cewa! 'Ya'yan da na goya sun tayar mini.


Kowane mutum da yake a duniya ya kasa kunne, kowannen da yake zaune a duniya, ya duba tutar, alama da za a ɗaga sama a ƙwanƙolin duwatsu, ya kasa kunne ga busar ƙaho!


Amma zaginsu ba zai yi mini ƙari ba, Gama Ubangiji Allah yana taimakona. Na ƙarfafa kaina domin in jure da su. Na sani ba zan kunyata ba,


Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa! Ki ji maganar Ubangiji!


Gama sun yi wauta a Isra'ila, sun yi zina da matan maƙwabtansu, sun yi ƙarya da sunana, ni kuwa ban umarce su ba. Ni na sani, ni ne kuma shaida, ni Ubangiji na faɗa.”


Sa'an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji mai gaskiya, mai aminci ya zama shaida a tsakaninmu, idan ba mu yi duk yadda Ubangiji Allahnka ya aiko ka gare mu ba.


Ki ji, ya ke duniya, Ga shi, ina kawo masifa a kan wannan jama'a, Sakayyar ƙulle-ƙullensu, Don ba su kula da maganata ba, Sun ƙi dokokina.


Sa'ad da na ji raina yana rabuwa da ni, Sai na tuna da kai, ya Ubangiji. Addu'ata kuwa ta kai gare ka a Haikalinka tsattsarka.


Su waɗanda suke yin sujada ga gumaka marasa amfani Sun daina yi maka biyayya.


“Amma Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Bari duniya ta yi tsit a gabansa.”


Kuna tambaya cewa, “Me ya sa ba ya karɓar hadayunmu?” Ai, domin ya sani ka keta alkawarin da ka yi wa matarka ta ƙuruciya ne, wadda ka ci amanarta ko da yake ita abokiyar zamanka ce, da matarka.


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”


“Ku saurara, ya ku sammai, gama zan yi magana, Bari duniya ta ji maganar bakina.


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, mutuwa ta biyu ba za ta cuce shi ba ko kaɗan.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ɓoyayyiyar manna, zan kuma ba shi wani farin dutse, da sabon suna a rubuce a jikin dutsen, ba kuwa wanda ya san sunan, sai wanda ya karɓe shi.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi izinin cin 'ya'yan itacen rai, wanda yake a cikin Firdausin Allah.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”


Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”


Suka amsa suka ce wa Yefta, “Ubangiji shi ne shaida tsakaninmu, lalle za mu yi maka kamar yadda ka ce.”


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan