Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Mattiyu 26:70 - Littafi Mai Tsarki

70 Amma ya musa a gabansu duka ya ce, “Ni ban san abin da kike nufi ba.”

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Sabon Rai Don Kowa 2020

70 Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Mattiyu 26:70
17 Iomraidhean Croise  

Wanda yake dogara ga son zuciyarsa, wawa ne, amma wanda yake tafiya cikin hikima zai kuɓuta.


Girmankan mutum zai jawo masa ƙasƙanci, amma za a girmama mai tawali'u.


Jin tsoron mutane tarko ne, amma wanda ya dogara ga Ubangiji za a ɗaukaka shi.


Ubangiji ya ce, “Wa ya sa ku fargaba, kuke jin tsoronsa, har kuka yi ƙarya? Ba ku tuna da ni, ko ku kula da ni ba? Ashe, ban yi haƙuri tun da daɗewan nan ba, duk da haka kuwa ba ku ji tsorona ba?


“Zuciya ta fi kome rikici, Cuta gare ta matuƙa, Wa zai san kanta?


Sai ga ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu ya miƙa hannu ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunne.


Amma duk wannan ya auku ne domin a cika littattafan annabawa.” Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.


Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin gidan babban firist. Da ya shiga, sai ya zauna tare da dogaran Haikali, don ya ga ƙarshen abin.


To, Bitrus kuwa yana zaune a tsakar gida a waje, sai wata baranya ta zo ta tsaya a kansa, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Yesu Bagalile!”


Da ya fito zaure, sai wata baranya kuma ta gan shi, ta ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Ai, mutumin nan tare yake da Yesu Banazare!”


Amma ya musa ya ce, “Ke, ban ma san shi ba.”


Hakika haka ne, amma saboda rashin bangaskiyarsu ne aka sare su, kai kuwa saboda bangaskiyarka ne kake kafe. Kada fa ka nuna alfarma, sai dai ka ji tsoron Allah.


Don haka duk wanda yake tsammani ya kahu, ya mai da hankali kada ya fāɗi.


Amma matsorata, da marasa riƙon amana, da masu aikin ƙyama, da masu kisankai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da kuma duk maƙaryata, duk rabonsu tafkin nan ne mai cin wuta da kibiritu, wanda yake shi ne mutuwa ta biyu.”


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan