Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -




Daniyel 6:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Dukan shugabannin ƙasar da masu mulki da muƙaddasai, da 'yan majalisa, da wakilai, sun tsai da shawara, cewa ya kamata sarki ya kafa doka, ya yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu'a ga wani gunki ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, sai a tura shi cikin kogon zakoki.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.

Faic an caibideil Dèan lethbhreac




Daniyel 6:7
25 Iomraidhean Croise  

Yakan jira a inda ya ɓuya kamar zaki. Yakan kwanta yana fakon wanda zai kama, Har ya kama shi da tarkonsa ya tafi da shi!


Sarakunan duniya sun yi tayarwa, Masu mulkinsu suna shirya maƙarƙashiya tare, Gāba da Ubangiji da zaɓaɓɓen sarkinsa.


Duba! Suna jira su auka mini, Mugaye suna taruwa gāba da ni, Ba domin wani zunubi ko wani laifin da na yi ba,


Ka tashi, ya Ubangiji, Allah Maɗaukaki, ka taimake ni, Ka tashi ka hukunta al'ummai, Kada ka yi wa waɗannan mugaye, maciya amana, jinƙai!


Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja, Kuna jin daɗin yin ƙarairayi. Kuna sa masa albarka, Amma a zuciyarku la'antarwa kuke yi.


Suka yarda a kan abin da suka shirya, Suka haɗa kai gāba da kai.


Ba ruwanka da alƙalai azzalumai, marasa gaskiya, Waɗanda suka mai da rashin gaskiya ita ce gaskiyarsu,


Sai Kaldiyawa suka yi magana da sarki da Aramiyanci, suka ce, “Ran sarki ya daɗe! Ka faɗa wa barorinka mafarkin, za mu kuwa yi maka fassararsa.”


Duk wanda bai fāɗi ƙasa ya yi sujada ba, za a jefa shi a tanderun gagarumar wuta.


Sa'an nan ya aika a kirawo su hakimai, da wakilai, da su muƙaddasai, da 'yan majalisa, da su ma'aji, da alƙalai, da masu mulki, da dukan ma'aikatan larduna, su zo, su halarci bikin keɓewar gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa.


Sa'an nan su hakimai, da wakilai, da muƙaddasai, da manyan 'yan majalisa suka taru, suka ga lalle wutar ba ta yi wa jikunan mutanen nan lahani ba, gashin kawunansu bai ƙuna ba, tufafinsu ba su ci wuta ba, ko warin wuta babu a jikinsu.


Duk wanda bai fāɗi ƙasa ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a tanderun gagarumar wuta.”


Sarki kuwa ya umarta a kawo Daniyel, a tura shi cikin kogon zakoki. Sarki kuma ya ce wa Daniyel, “Ina fata Allahn nan wanda kake bauta masa kullum zai cece ka.”


Allahna ya aiko mala'ikansa ya rufe bakunan zakoki, ba su iya yi mini lahani ba, domin ban yi wa Allah laifi ba, ban kuma yi maka ba.”


Ya ku jama'ata, ku tuna Da abin da Balak, Sarkin Mowab, ya ƙulla, Da yadda Bal'amu ɗan Beyor ya amsa masa, Da abin da ya faru daga Shittim, har zuwa Gilgal, Don ku san ayyukan adalci na Ubangiji.”


Zaki ya kashe abin da ya ishi kwiyakwiyansa. Ya kaso wa zakanyarsa abin da ya ishe ta. Ya cika kogonsa da ganima.


Amma Farisiyawa suka fita, suka yi shawara a kansa, yadda za su hallaka shi.


Suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci su kashe shi.


Da wayewar gari sai manyan firistoci da shugabanni, da malaman Attaura, da dukkan 'yan majalisa suka yi shawara. Sai suka ɗaure Yesu, suka tafi da shi, suka ba da shi ga Bilatus.


Sai manyan firistoci suka yi shawarar kashe Li'azaru, shi ma,


Lean sinn:

Sanasan


Sanasan