Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -

Zabura 87 - Littafi Mai Tsarki


Fa'idar Zama a Urushalima

1 Allah ya gina birninsa a bisa tsarkakan tuddai,

2 Yana ƙaunar birnin Urushalima fiye da kowane wuri a Isra'ila.

3 Ya birnin Allah, ka kasa kunne, Ga abubuwan banmamaki da ya faɗa a kanka.

4 “Sa'ad da na lasafta sauran al'umma da suke yi mini biyayya, Zan sa Masar da Babila a cikinsu, Zan ce da Filistiya, da Taya, da Habasha, Su ma na Urushalima ne.”

5 A kan Sihiyona kuwa za a ce, “Dukan sauran al'umma nata ne.” Maɗaukaki kuwa zai ƙarfafa ta.

6 Ubangiji zai rubuta lissafin jama'o'i, Ya sa su duka cikin jimilla ta Urushalima.

7 Duk mazauna a wurin za su raira waƙa, su yi rawa, Su ce, “Dukan maɓuɓɓugaina suna cikinka.”

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
Lean sinn:



Sanasan