Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -

Zabura 141 - Littafi Mai Tsarki


Addu'ar Maraice ta Neman Keɓewa daga Mugunta

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Ka taimake ni yanzu! Ka saurare ni sa'ad da na kira gare ka.

2 Ka karɓi addu'ata kamar turaren ƙonawa, Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice.

3 Ya Ubangiji, ka sa a yi tsaron bakina, Ka sa mai tsaro a leɓunana.

4 Ka tsare ni daga son yin mugunta, Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu, Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu!

5 Nagarin mutum ya iya hukunta ni, ya tsauta mini da alheri, Zai zamar mini kamar an shafe kaina da mai, Domin kullayaumi ina addu'a gāba da mugayen ayyuka.

6 Mutane za su yarda, cewa maganata gaskiya ce, Sa'ad da aka jefo da masu mulkinsu ƙasa, daga ƙwanƙolin dutse,

7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse, Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari.

8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka, Ina neman kiyayewarka, Kada ka bar ni in halaka!

9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini, Daga ashiftar masu aikata mugunta.

10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu, Ni kuwa in zo in wuce lafiya.

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
Lean sinn:



Sanasan