Biblia Todo Logo
Bìoball air-loidhne

- Sanasan -

Ayuba 25 - Littafi Mai Tsarki


Bildad Bai Yarda Allah Zai Baratar da Mutum Ba

1 Bildad ya amsa.

2 “Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa, A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama.

3 Akwai wanda zai iya ƙidaya mala'ikun da suke masa hidima? Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?

4 Akwai wanda ya isa ya zama adali, Ko mai tsarki a gaban Allah?

5 Hasken wata ba haske ba ne a gare shi, Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa.

6 To, mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah?”

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
Lean sinn:



Sanasan